Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji
Published: 26th, March 2025 GMT
Ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru, ya ziyarci Cibiyar Horar da Sojoji da ke Zariya, inda ya yi alƙawarin samar da ƙarin kayan aiki da ci gaba da inganta horon kuratan sojoji domin su dace da buƙatun zamani.
A lokacin ziyarar, Ministan ya bayyana gamsuwarsa da horon da kurata na kashi 88 ke samu, inda ya jaddada aniyar Gwamnatin Tarayya na bunƙasa kayan horo da samar da ingantattun makamai da kayan aiki ga dakarun sojoji.
Badaru ya yi alƙawarin tuntuɓar Gwamnatin Jihar Kaduna, domin kammala ginin Makarantar Sakandaren Chindit, wadda ba a kammala ta ba tsawon lokaci.
Ya kuma bayar da tabbacin samar wa Makarantar Firamare ta Chindit kayan aiki domin inganta ilimin ’ya’yan sojojin da ke barikin.
Baya ga haka, ministan ya amince da samar da rijiyoyin burtsatse a barikin, domin shawo kan matsalar ƙarancin ruwa da ake fuskanta a Depot Zariya.
A jawabinsa na maraba, Kwamandan Depot, Manjo Janar Ahmadu Mohammed, ya gode wa ministan bisa wannan ziyarar, tare da bayyana yadda Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ke ba su goyon baya domin magance matsalolinsu.
Ya kuma bayyana cewa za su ci gaba da samar da ƙwararrun sojoji masu kishin ƙasa da jajircewa.
Ziyarar ministan ta samu rakiyar manyan jami’an tsaro, ciki har da Babban Sakataren Ma’aikatar Tsaro, Jakada Gabriel Aduda, da Manjo Janar Ahmed Jubrin (mai ritaya), da kuma Birgediya Janar Aminu Garba.
Hakazalika, wasu manyan hafsoshin soji irin su Kwamandan Armed Forces Command and Staff College, Air Marshal Hassan Alhaji, da Kwamandan Makarantar Motsa Jiki ta Sojojin Najeriya, Birgediya Janar Owoicho Ejiga, na cikin tawagar.
Ziyarar na daga cikin ƙoƙarin ministan na ganin an inganta cibiyoyin horon sojoji domin tabbatar da nagartar jami’an tsaro a Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alƙawari Cibiyar Horar Da Sojoji kayan aiki Ministan tsaro Mohammed Badaru Zariya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
Wasu mutum shida sun shiga hannun ’yan sanda kan zargin satar zinari da kuɗinta ya haura Naira miliyan 109.5 a Jihar Kebbi.
Sashen binciken manyan laifuka na rundunar ’yan sanda a jihar Kebbi na tuhumar su da sace sarkoƙin zinare guda biyar sauran kayan zinare daga wani gida a garin Ka’oje, Ƙaramar Hukumar Bagudo.
Sauran sun haɗa da zobba huɗu da munduwar hannu tara, da nauyinsu ya kai gram 782.7 — dukkansu mallakar ’ya’ya da ’yan uwar mai gidan.
Wanda ake tuhuma ya amsa laifiBayan samun koken, jami’an suka kama Ibrahim Abubakar Ka’oje, jami’i a Hukumar Gyaran Hali ta Kasa, wanda a yayin bincike, ya amsa laifin.
’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhuYa bayyana cewa ya sayar da kayan ga wasu mutane biyu, dukkansu daga Sakkwato, tare da wasu mutum biyu a Jihar Kebbi.
An kuma gano wanda ya taimaka masa wajen sayar da wasu daga cikin kayan, inda ya karɓi naira miliyan 2.5 a matsayin lada.
Rundunar ’yan sanda ta bayyana cewa har yanzu tana neman sauran da suka gudu, bisa zargin taimakawa wajen sayar da kayan sata.
Ana zargin an sayi filaye biyu a Birnin Kebbi da kuɗin da aka samu daga sayar da kayan.
Abubuwan da aka ƙwatoKayan da aka ƙwato sun haɗa da munduwar hannu biyu, babur ɗin Haouje, da kuma wayoyin iPhone 16, Samsung Galaxy Ultra da Samsung Flip.
Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Kebbi, Bello M. Sani, ya jinjina wa jajircewar jami’ansa bisa wannan nasara.
Ya kuma yi kira gare su da su ci gaba da aiki tukuru domin cafke sauran da ake nema da kuma ƙwato dukkan kayan da suka rage.