Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji
Published: 26th, March 2025 GMT
Ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru, ya ziyarci Cibiyar Horar da Sojoji da ke Zariya, inda ya yi alƙawarin samar da ƙarin kayan aiki da ci gaba da inganta horon kuratan sojoji domin su dace da buƙatun zamani.
A lokacin ziyarar, Ministan ya bayyana gamsuwarsa da horon da kurata na kashi 88 ke samu, inda ya jaddada aniyar Gwamnatin Tarayya na bunƙasa kayan horo da samar da ingantattun makamai da kayan aiki ga dakarun sojoji.
Badaru ya yi alƙawarin tuntuɓar Gwamnatin Jihar Kaduna, domin kammala ginin Makarantar Sakandaren Chindit, wadda ba a kammala ta ba tsawon lokaci.
Ya kuma bayar da tabbacin samar wa Makarantar Firamare ta Chindit kayan aiki domin inganta ilimin ’ya’yan sojojin da ke barikin.
Baya ga haka, ministan ya amince da samar da rijiyoyin burtsatse a barikin, domin shawo kan matsalar ƙarancin ruwa da ake fuskanta a Depot Zariya.
A jawabinsa na maraba, Kwamandan Depot, Manjo Janar Ahmadu Mohammed, ya gode wa ministan bisa wannan ziyarar, tare da bayyana yadda Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ke ba su goyon baya domin magance matsalolinsu.
Ya kuma bayyana cewa za su ci gaba da samar da ƙwararrun sojoji masu kishin ƙasa da jajircewa.
Ziyarar ministan ta samu rakiyar manyan jami’an tsaro, ciki har da Babban Sakataren Ma’aikatar Tsaro, Jakada Gabriel Aduda, da Manjo Janar Ahmed Jubrin (mai ritaya), da kuma Birgediya Janar Aminu Garba.
Hakazalika, wasu manyan hafsoshin soji irin su Kwamandan Armed Forces Command and Staff College, Air Marshal Hassan Alhaji, da Kwamandan Makarantar Motsa Jiki ta Sojojin Najeriya, Birgediya Janar Owoicho Ejiga, na cikin tawagar.
Ziyarar na daga cikin ƙoƙarin ministan na ganin an inganta cibiyoyin horon sojoji domin tabbatar da nagartar jami’an tsaro a Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alƙawari Cibiyar Horar Da Sojoji kayan aiki Ministan tsaro Mohammed Badaru Zariya
এছাড়াও পড়ুন:
EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza
Kungiyar tarayyar Turai tana shirin jingine aiki da HKI na wani lokacin, a cibiyoyin binciken ilmin da suke da su a nahiyar ta Turai saboda ayyukan kissan kare dangi da kuma hana abinci shiga gaza da take yi.
Tashar talabijan da Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar EU tana fadar haka, ta kuma kara da cewa kasashen turai sun gargadi HKI da ta daina hana abinci shiga gaza, amma ta yi taurine kai. Don haka a halin yanzu majalisar gudanar da na kungiyar tana shirin haramtawa HKI amfanina da wani bangare na ayyukan bincike na kasashen kungiyar, musamman wadanda suka shafi kirkirenren fasaha wato AI don kada ta yi amfani da su wajen yakar falasdinawa a gaza da ita.
Wannan shi ne karon farko wanda tarayyar Turai take daukan wani mataki, wanda shima bai taka kara ya karya ba, kan HKI.
Amma tun lokacinda aka fara yakin a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 mafi yawan kasashen turai musamman kuma kasashen Jamus da Burtania suna goyon bayan HKI, suna kuma tallafa mata da makamai don ci gaba da kissan Falasdinawa a Gaza. A yanzu al-amarin ya kaiga duniya gaba daya ta tabbatar da cewa abinda HKI take yi a Gaza kisan kiyashi ne, sai suka ce bari su yi wani abu, wanda zai zama hajjace ta kare kansu idan an ce basu yi kome ba. Amma duk da haka kungiyar tarayyar Turai tana tare da HKI 100% kan kissan Falasdinawa a Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025 Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai July 29, 2025 Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu July 29, 2025 Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta July 29, 2025 Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba July 29, 2025 Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta July 29, 2025 Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza July 29, 2025 Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine July 29, 2025 Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci