Aminiya:
2025-06-14@21:50:00 GMT

Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji

Published: 26th, March 2025 GMT

Ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru, ya ziyarci Cibiyar Horar da Sojoji da ke Zariya, inda ya yi alƙawarin samar da ƙarin kayan aiki da ci gaba da inganta horon kuratan sojoji domin su dace da buƙatun zamani.

A lokacin ziyarar, Ministan ya bayyana gamsuwarsa da horon da kurata na kashi 88 ke samu, inda ya jaddada aniyar Gwamnatin Tarayya na bunƙasa kayan horo da samar da ingantattun makamai da kayan aiki ga dakarun sojoji.

Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasu Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku

Badaru ya yi alƙawarin tuntuɓar Gwamnatin Jihar Kaduna, domin kammala ginin Makarantar Sakandaren Chindit, wadda ba a kammala ta ba tsawon lokaci.

Ya kuma bayar da tabbacin samar wa Makarantar Firamare ta Chindit kayan aiki domin inganta ilimin ’ya’yan sojojin da ke barikin.

Baya ga haka, ministan ya amince da samar da rijiyoyin burtsatse a barikin, domin shawo kan matsalar ƙarancin ruwa da ake fuskanta a Depot Zariya.

A jawabinsa na maraba, Kwamandan Depot, Manjo Janar Ahmadu Mohammed, ya gode wa ministan bisa wannan ziyarar, tare da bayyana yadda Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ke ba su goyon baya domin magance matsalolinsu.

Ya kuma bayyana cewa za su ci gaba da samar da ƙwararrun sojoji masu kishin ƙasa da jajircewa.

Ziyarar ministan ta samu rakiyar manyan jami’an tsaro, ciki har da Babban Sakataren Ma’aikatar Tsaro, Jakada Gabriel Aduda, da Manjo Janar Ahmed Jubrin (mai ritaya), da kuma Birgediya Janar Aminu Garba.

Hakazalika, wasu manyan hafsoshin soji irin su Kwamandan Armed Forces Command and Staff College, Air Marshal Hassan Alhaji, da Kwamandan Makarantar Motsa Jiki ta Sojojin Najeriya, Birgediya Janar Owoicho Ejiga, na cikin tawagar.

Ziyarar na daga cikin ƙoƙarin ministan na ganin an inganta cibiyoyin horon sojoji domin tabbatar da nagartar jami’an tsaro a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alƙawari Cibiyar Horar Da Sojoji kayan aiki Ministan tsaro Mohammed Badaru Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara

Dakarun sojin Nijeriya sun yi nasarar kashe wasu ’yan ta’adda yayin wani samame da suka kai garin Kunchin Kalgo a ƙaramar hukumar Tsafe da ke Jihar Zamfara.

A sanarwar da rundunar ta wallafa a shafinta na X ranar Alhamis, ta ce a ranar 10 ga watan Yuni ne rundunar FANSAN YAMMA ta kashe ƙasurguman ‘yan ta’addan da suka haɗa da Auta da Abdul Jamilu da kuma Salisu.

Leroy Sane ya koma Galatasaray Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu

“Waɗannan ’yan ta’adda suna da alaƙa da ayyukan tashin hankali da ta’addanci da ake yawan samu a yankin gaba ɗaya.

“Wannan farmakin dai na nuni da wani gagarumin koma baya ga masu aikata laifuka, wanda ke dagula zaman lafiya da tsaro a yankin,” in ji sanarwar.

Bayanan sirri na farko-farko sun nuna cewa an kashe ƙarin wasu shugabannin ’yan ta’adda, ciki har da wani da aka fi sani da Babaye a lokacin harin.

Kazalika, a wani lamarin daban, rahotanni sun ce an kashe Sale Ado Madele da aka fi sani da Sarki, babban ɗan shugaban ‘yan bindiga Ado Alieru.

A wani lamarin mai kama da haka, sojojin sun kuma kashe wasu ’yan ta’adda goma da suka taru a kusa da wata tashar mai da ke garin Danjibga.

Ana kyautata zaton ‘yan ta’addan na cikin wani gungun hadin-gwiwa da Dogo Sule ya haɗa domin kai hari.

Rundunar sojojin Nijeriya ta ce tana ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da kuma maido da dauwamammen zaman lafiya a fadin Jihar Zamfara da yankin Arewa maso Yamma.

“Wannan aiki yana ƙara jaddada ƙudurinmu na wargaza hanyoyin sadarwar ‘yan ta’adda tare da gurfanar da masu aikata laifuka a gaban ƙuliya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
  • Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar