Kwamishinan tsaron cikin gida da ayyuka na musamman na jihar Kano, Manjo Janar Muhammad Inuwa Idris (mai ritaya), ya yi murabus daga mukaminsa. An tabbatar da murabus din nasa ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar. Ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da murabus din a hukumance, inda ya nuna jin dadinsa da irin gudunmawar da Janar din sojan ya bayar a lokacin da yake gudanar da aikinsa.

Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea Kasuwar Kayayyakin Masarufi Ta Sin Za Ta Ci Gaba Da Nuna Yanayin Bunkasa Bisa Daidaito A Bana LEADERSHIP ta ruwaito cewa, Manjo janar Idris (mai ritaya) shi ne mamba na biyu a majalisar zartarwa ta jihar Kano da ya mika takardar murabus dinsa a shekarar 2025. In ba a manta ba, kwamishinan sa ido da tantance ayyuka, Mohammed Diggol, shi ma ya yi murabus a farkon wannan shekarar. An nada Manjo Janar Idris ne a watan Agustan 2024 a matsayin kwamishinan sabuwar ma’aikatar da aka kirkiro. A cikin dan kankanin wa’adinsa, ya taka muhimmiyar rawa wajen kafa tsarin gudanar da ayyukan ma’aikatar. A cikin sanarwar a hukumance, gwamna Yusuf ya yabawa Manjo janar Idris bisa jajircewarsa da yi wa jihar hidima. “Muna godiya ga Manjo Janar Muhammad Inuwa Idris (mai ritaya) bisa jajircewa da bayar da gudunmawa wajen ci gaban jihar Kano tun daga lokacin da ya ke aikin soja, muna masa kyakkyawan fata a cikin sabuwar rayuwarsa ta gaba,” in ji gwamnan. Duk da cewa ba a bayar da wani dalili na murabus din nasa na ba zato ba tsammani ba, gwamnan ya bayyana kwarin gwiwar cewa, magajinsa zai dora kan harsashin da Idris ya kafa domin ganin ma’aikatar ta yi aiki yadda ya kamata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗa Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a matsayin sabon Sarkin Gusau kuma Sarkin Katsina na Masarautar Gusau.

Sakataren Gwamnatin Jihar Zamfara, Malam Abubakar Mohammad Nakwada ne ya sanar da hakan, inda ya bayyana cewa an yi naɗin ne bisa ga shawarwarin da masu zaɓen sarakuna na masarautar Gusau suka bayar, tare da bin al’ada da dokokin da suka dace.

A wata sanarwa da mai taimakawa na musamman kan harkokin yaɗa labarai a ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Zamfara, Sulaiman Ahmad Tudu, ya fitar, ya ce sabon Sarkin, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello, shi ne ɗa na farko ga marigayi Sarki, kuma kafin naɗin nasa yana riƙe da mukamin Bunun Gusau.

Alhaji Abdulkadir ya hau karagar mulki a matsayin Sarkin Gusau na 16, bayan rasuwar mahaifinsa, Mai Martaba Dokta Ibrahim Bello, wanda ya rasu a ranar 25 ga Yulin 2025, bayan shafe shekara goma yana mulki.

Yayin da yake taya sabon sarkin murna, Gwamna Lawal ya bukace shi da ya ci gaba da rike kyakkyawar jagoranci da mutumtaka da aka san kakanninsa da shi, musamman kasancewarsa  tsatson Malam Sambo Dan Ashafa.

Gwamnan ya kuma bukaci sabon Sarkin da ya kasance jajirtacce wajen kawo haɗin kai, zaman lafiya da cigaba, tare da ƙarfafa hadin kai  a ciki da wajen masarautar Gusau.

 

Daga Aminu Dalhatu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan