Gwamnatin Kano za ta hukunta masu shigar banza a bikin Sallah
Published: 26th, March 2025 GMT
Gwamnatin Kano ta sha alwashin hukunta masu shigar banza ko cudanya maza da mata a lokacin bukukuwan Sallah Karama da za a yi.
Gwamnatin ta bayyana hakan ne ta bakin shugaban Hukumar Tace Fina-finai da Dab’i ta Kano, Abba Almustapha a wata sanarwa da ta fitar mai dauke da sa hannun kakakin hukumar Abdullahi Sani Sulaiman, inda ta ce matakin yunkuri ne na gwamnatin domin tsaftace yadda gidajen wasanni da kidan DJ ke shagalin bikin Sallah.
“A kokarin ta na yaki da rashin da’a tare tsaftace yadda gidajen wasanni da masu kidan DJ za su gudanar da shagalin bikin sallah a Kano, Hukumar tace fina-finai da Dab’i karkashin jagorancin Abba El-mustapha ta bayyana shirinta na saka kafar wando daya da duk wani gidan wasa ko mai kidan DJ da aka samu da rashin da’a a yayin gudanar da bikin sallah a Jihar.
Hukumar ta shirya wata tawaga ta musamman da za ta kewaya gidajen wasannin a bikin sallah karkashin kulawar Alh. Abubakar Zakari Garun Babba Daraktan Dab’i na Hukumar, domin sanya ido da tabbatar ba a bai wa masu shigar banza ko shaye – shaye damar shiga gidajen wasannin ba.
“Haka kuma, hukumar ta hana hada maza da mata a guri daya a yayin bikin sallar. Tawagar za ta yi aiki ne dare da rana daga ranar daya ga sallah har zuwa lokacin da za’a kammala bikin sallar domin cimma nasarar aikin da ta sanya a gaba.”
El-mustapha ya kuma yi gargadi ga masu gidajen wasanni da masu sana’ar DJ, da su yi biyayya ga dokokin hukumar sau da kafa domin gujewa fushinta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar Tace Fina finai da Dab I ta Kano Kannywod
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
A wani bayani na hadin gwiwa da hukumar makamashin Nukiliya ta Iran da kuma ma’aikatar harkokin wajen Iran su ka fitar, sun bayar da umarnin a bude wani wuri na daban na sirri domin ci gaba da tace sanadarin Urani’um, sannan kuma a maye gurbin bututu tace sanadarin mai mataki na daya, da mai mataki na shida a cibiyar “Pardo.”
Bayanin dai ya zo ne a matsayin mayar da martani ga sanarwar da ta fito daga kwamitin alkalai na hukumar makamashin Nukiliya ta kasa da kasa akan Iran.
Bugu da kari, bayanin na Iran ya kuma ce; A kodayaushe jamhuriyar musulunci ta Iran tana aiki da nauyin da ya rataya a wuyanta, kuma har ya zuwa yanzu babu wani rahoto na hukumar wanda ya bayyana cewa; Iran ba ta aiki da ka’idojin hana yaduwar makaman Nukiliya.”
Haka nan kuma bayanin ya ambaci cewa; Tare da cewa Iran tana daukar rahoton da cewa na siyasa ne, wanda Amurka da kasashen turai suke amfani da hukumar a matsayin makami, ba tare da dogaro da wani dalili na ilimi ba.
Har ila yau Iran din ta zargi Amurka da kasashen na turai da wuce gona da iri wajen tsara rahoton da yake cin karo da rahoton da shugaban hukumar ta makamashin Nukiliya ya fitar, wanda bai sami wani abu mai shiga duhu ba a cikin Shirin na Iran na zama lafiya.