HausaTv:
2025-07-30@17:45:27 GMT

Sudan: RSF ta hana kayan agaji a yankunan da ke a karkashin ikonta

Published: 26th, March 2025 GMT

Dakarun (RSF) sun sanya sabbin takunkumai kan isar da kayan agaji a yankunan da ke karkashin ikonsu, lamarin da ya kara ta’azzara matsalar ayyukan jin kai, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

Matsalolin dai na zuwa ne a daidai lokacin da kungiyar RSF ke kokarin kafa gwamnatin daga bangarenta a yammacin kasar ammacin Sudan, duk da fatattakarsu sojojin kasar suka yi daga  babban birnin kasar, Khartoum, lamarin da ke barazana ga rarrabuwar kawuna a kasar da yaki ya daidaita.

Matakan da kungiyar ta dauka na hana gudanar da ayyukan agaji na barazana ga rayuwar dubban daruruwan mutane a yankin na Darfur, wadanda da dama daga cikinsu sun riga sun rasa matsugunansu sakamakon tashe-tashen hankula a baya.

A baya ma’aikatan agaji sun zargi mayakan RSF da wawushe kayan agaji a tsawon fiye da shekaru biyu da ake fama da tashin hankali a Sudan, lamarin da ke kara ta’azzara yunwa da cututtuka a  kasar.

Ma’aikatan agaji goma sha biyu, da suka yi magana da kamfanin dillancin labarai na Reuters, sun ce tun a karshen shekarar da ta gabata, kungiyar ta RSF ta fara neman karin kudade da kuma sa ido kan yadda ake gudanar da ayyuka, kamar daukar ma’aikatan cikin gida da tsaro, da irin tsarin da hukumomin da ke da alaka da sojoji ke amfani da su, da kuma kara tsaurara hanyoyin shiga.

A baya dai ba a bayar da rahoton wannan yunkuri na RFS ba,  amma kungiyoyin agaji na kasa da kasa sun fara ja da baya sakamakon matsanancin yanayin da ake ciki.

A cewar ma’aikatan agaji, yunƙurin da RSF ke yi ya kawo babban cikas ga ayyukansu, wanda ke nuni da yiwuwar fadawar miliyoyion mutane a cikin matsanancin hali na yunwa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Babbar hukumar kwastam ta Sin ta fitar da sanarwar a yau Talata cewa, shirin amincewa da juna na tsarin “Masu gudanar da kamfanoni da aka ba su izni” wato AEO a takaice tsakanin Sin da Benin da Thailand zai fara aiki a hukumance daga ranar 1 ga watan Agustan shekarar 2025.

Bayan aiwatar da wannan tsarin amincewa da juna, za a ba da dama tsakanin kwastam na Sin da na Benin, da kuma kwastam na Sin da na Thailand, don su amince da juna a karkashin AEO.

Bugu da kari, yayin da ake tantance kayayyakin da ake shigowa da su daga waje a wurin kwastam, za a saukaka wa kamfanonin dake karkashin tsarin AEO wasu abubuwa, kamar rage yawan matakan dubawa, da ba su fifiko kan ayyukan kwastam, da kuma kebe musu jami’an hulda na kwastam da sauran matakai na samun sauki.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza
  • Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Kungiyar Gwamnonin Jihohi Ta Jajintawa Jihar Adamawa Bisa Ambaliyar Ruwa A Yola
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata
  • Taron ‘Kasashe biyu’ A Gefen Taron MDD A NewYork