Sudan: RSF ta hana kayan agaji a yankunan da ke a karkashin ikonta
Published: 26th, March 2025 GMT
Dakarun (RSF) sun sanya sabbin takunkumai kan isar da kayan agaji a yankunan da ke karkashin ikonsu, lamarin da ya kara ta’azzara matsalar ayyukan jin kai, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.
Matsalolin dai na zuwa ne a daidai lokacin da kungiyar RSF ke kokarin kafa gwamnatin daga bangarenta a yammacin kasar ammacin Sudan, duk da fatattakarsu sojojin kasar suka yi daga babban birnin kasar, Khartoum, lamarin da ke barazana ga rarrabuwar kawuna a kasar da yaki ya daidaita.
Matakan da kungiyar ta dauka na hana gudanar da ayyukan agaji na barazana ga rayuwar dubban daruruwan mutane a yankin na Darfur, wadanda da dama daga cikinsu sun riga sun rasa matsugunansu sakamakon tashe-tashen hankula a baya.
A baya ma’aikatan agaji sun zargi mayakan RSF da wawushe kayan agaji a tsawon fiye da shekaru biyu da ake fama da tashin hankali a Sudan, lamarin da ke kara ta’azzara yunwa da cututtuka a kasar.
Ma’aikatan agaji goma sha biyu, da suka yi magana da kamfanin dillancin labarai na Reuters, sun ce tun a karshen shekarar da ta gabata, kungiyar ta RSF ta fara neman karin kudade da kuma sa ido kan yadda ake gudanar da ayyuka, kamar daukar ma’aikatan cikin gida da tsaro, da irin tsarin da hukumomin da ke da alaka da sojoji ke amfani da su, da kuma kara tsaurara hanyoyin shiga.
A baya dai ba a bayar da rahoton wannan yunkuri na RFS ba, amma kungiyoyin agaji na kasa da kasa sun fara ja da baya sakamakon matsanancin yanayin da ake ciki.
A cewar ma’aikatan agaji, yunƙurin da RSF ke yi ya kawo babban cikas ga ayyukansu, wanda ke nuni da yiwuwar fadawar miliyoyion mutane a cikin matsanancin hali na yunwa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Ondo ta tabbatar da kama wata mata mai suna Iluyemi Bosede bisa zargin kashe yayarta, Tewogboye Omowumi, a Akure, babban birnin jihar.
A cewar sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Olayinka Ayanlade, ya fitar a ranar Talata, ya ce lamarin ya faru ne a ranar shida ga Satumba, 2025, bayan wata sa’insa da ta kaure tsakanin matar da marigayiyar kan Naira 800.
Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin NajeriyaJami’in ya bayyana cewa Bosede ta ture ’yar uwarta har ta faɗi ƙasa, lamarin da ya haifar da mutuwarta.
Ya ce, “Binciken farko ya nuna cewa Iluyemi Bosede ta je wurin yayar tata, Tewogboye Omowumi mai shekaru 35, domin karbar bashinta na N800 na kudin tumatir da barkono. Sai dai tankiyar da ta fara a matsayin ƙaramin sabani ta rikide zuwa tashin hankali, inda ake zargin Bosede ta riƙe kayan marigayiyar har ta faɗi ƙasa.”
“Abin takaici, duk da an garzaya da marigayiyar asibiti don samun kulawar gaggawa, likitoci sun tabbatar da mutuwarta tun kafin a fara ba ta taimako. Wannan lamari ya nuna yadda ƙaramin sabani zai iya rikidewa zuwa mummunar husuma idan ba a magance shi cikin lumana ba.”
Bayan faruwar lamarin, rundunar ta ce ta kama wadda ake zargi kuma tana tsare da ita a halin yanzu, yayin da bincike ke ci gaba.
Rundunar ta kuma tabbatar da cewa za a gurfanar da wadda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike, domin ta girbi abin da ta shuka.