Jigawa Ta Bude Sabon Babi: Maniyyata Za Su San Masaukansu Tun Daga Gida Najeriya
Published: 25th, April 2025 GMT
Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta bullo da tsarin da kowanne maniyyaci zai san masaukinsa a kasa mai tsarki tun daga nan gida najeriya.
Shugaban hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a shalkwatar hukumar dake Dutse.
Yana mai cewar, wannan shi ne karon farko da hukumar ta bullo da tsarin domin maniyyaci ya san masaukinsa a nan gida kafin zuwa kasa mai tsarki.
Game da batun kudade kuwa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma kaddamar da kwamitin canjin kudaden guzuri na maniyyata domin samun saukin canji yayin aikin Hajjin.
Ya ce an kafa kwamitin ne domin bibiyar maniyyata kan canjin kudin guzuri, kasancewar wasu batagari na damfarar mahajjata a kasa mai tsarki wajen canjin kudade daga Dala zuwa Riyal.
Ya kara da cewar, hukumar ta turawa hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON fiye da naira miliyan dubu shida da miliyan dari uku da talatin da daya (6,331,000,000) a matsayin kudaden maniyyatan aikin hajjin bana.
Ya ce jihar Jigawa ce ta farko wajen biyan kudaden aikin hajjin bana ga hukumar aikin hajji ta kasa.
Ahmed Umar Labbo ya kara da cewar Gwamnatin jihar ta baiwa hukumar rancen naira miliyan dubu uku da miliyan dari uku da sittin (3,360,000,000) da ta yi amfani da shi wajen sayen kujerun aikin hajjin bana daga hukumar aikin hajji ta kasa.
Umar Labbo, ya ce sun cimma kaso 95 bisa 100 na aikin bada biza ga maniyyata.
Babban Daraktan ya shedawa mahalarta taron cewar hukumar ta kammala duk wani shiri na fara jigilar maniyatan wanda za a fara jigilar alhazan Najeriya a ranar tara ga watan Mayu.
Kazalika, wakilan hukumomin tsaro sun yi bayani akan shirye shiryen da suke yi domin tunkarar aikin hajjin bana
Ya kuma yi kira ga maniyyatan jihar, da su ci gaba da halartar cibiyoyin bita domin samun ilimin da za su gudanar da aikin hajji cikin sauki.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta ce Najeriya na rasa sama da Dala Biliyan 10 duk shekara sakamakon asarar amfanin gona bayan girbi.
Ministan Noma Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a wajen kaddamar da shirin Hanyar Inganta Noma da Kayayyakin Mire Rayuwa a Yankunan Karkara G.R.A.I.N a ƙaramar hukumar Birnin Kudu ta Jihar Jigawa.
Ya ce asarar na faruwa ne saboda rashin ingantattun wuraren ajiya, karancin ababen more rayuwa, sauyin yanayi da kuma ambaliya.
Kyari ya bayyana cewa noma na bada gudunmawar kashi 24 bisa 100 na Jimillar Darajar Kayayyaki da Ayyuka da Kasa ta Samar a Cikin Shekara GDP, inda ƙananan manoma ke samar da sama da kashi 70 bisa 100 na abincin da ake ci a ƙasa.
Ya jaddada cewa gwamnati za ta tallafa musu da kayan noma na zamani da wuraran kasuwanci domin inganta tattalin arziki.
A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi na Jigawa ya yaba da samun Cibiyar Cigaban Karakara ta Pulse ta farko a Jigawa, yana mai cewa za ta kawo sauyi a harkar noma da rayuwar jama’ar karkara.
Haka zalika, shi ma Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu zai taimaka wajen ci gaban tattalin arziki.
Shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kudu, Alhaji Builder Muhammad Uba, ya jaddada goyon bayansa ga shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Tinubu tare da yabawa gwamnatin Namadi kan sauya fasalin noma a jihar.
Usman Muhammad Zaria