Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta bullo da tsarin da kowanne maniyyaci zai san masaukinsa a kasa mai tsarki tun daga nan gida najeriya.

Shugaban hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a shalkwatar hukumar dake Dutse.

Yana mai cewar, wannan shi ne karon farko da hukumar ta bullo da tsarin domin maniyyaci ya san masaukinsa a nan gida kafin zuwa kasa mai tsarki.

Game da batun kudade kuwa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma kaddamar da kwamitin canjin kudaden guzuri na maniyyata domin samun saukin canji yayin aikin Hajjin.

Ya ce an kafa kwamitin ne domin  bibiyar maniyyata kan canjin kudin guzuri, kasancewar wasu batagari na damfarar mahajjata a kasa mai tsarki wajen canjin kudade daga Dala zuwa Riyal.

Ya kara da cewar, hukumar ta turawa hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON fiye da naira miliyan dubu shida da miliyan dari uku da talatin da daya (6,331,000,000) a matsayin kudaden maniyyatan aikin hajjin bana.

Ya ce jihar Jigawa ce ta farko wajen biyan kudaden aikin hajjin bana ga hukumar aikin hajji ta kasa.

Ahmed Umar Labbo ya kara da cewar Gwamnatin jihar ta baiwa hukumar rancen naira miliyan dubu uku da miliyan dari uku da sittin (3,360,000,000) da ta yi amfani da shi wajen sayen kujerun aikin hajjin bana daga hukumar aikin hajji ta kasa.

Umar Labbo, ya ce sun cimma kaso 95 bisa 100 na aikin bada biza ga maniyyata.

Babban Daraktan ya shedawa mahalarta taron cewar hukumar ta kammala duk wani shiri na fara jigilar maniyatan  wanda za a fara jigilar alhazan Najeriya a ranar tara ga watan Mayu.

Kazalika, wakilan hukumomin tsaro sun yi bayani akan shirye shiryen da suke yi domin tunkarar aikin hajjin bana

Ya kuma yi kira ga maniyyatan jihar, da su ci gaba da halartar cibiyoyin bita domin samun ilimin da za su gudanar da aikin hajji cikin sauki.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa

Jirgin Fadar Shugaban Kasa da Gwamnatin Najeriya ta saka a kasuwa da nufin sayarwa ya kasa samun mai saye kusan watanni biyar bayan ɗora shi a dandalin sayar da jiragen sama na duniya.

A sakamakon haka, tuni ma kamfanin dillancin da ke kula da sayar da jirgin samfurin Boeing 737-700 Business Jet ya janye jerin sayar da shi daga shafinsa.

’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe

Jaridar Punch ta rawaito cewa jirgin da a baya aka saka a shafin kamfanin, yanzu an cire shi daga kai.

A cikin wata amsa ga sakon imel, Laurie Barringer wanda shi ne Manajan Binciken Kasuwa na JetHQ, ya tabbatar da cewa kamfanin ya cire jirgin daga jerin sayarwa, inda ya ce a nemi karin bayani daga Gwamnatin Najeriya.

“Mun gode da sakonku. Ba mu da jerin Boeing yanzu a shafinmu. Sai dai ku tuntubi Gwamnatin Najeriya don samun bayani kan abin da ya faru da jirgin. Na gode da lokacinku — Laurie Barringer, Manajan Binciken Kasuwanci, JetHQ,” in ji sakon.

Hadimin Mai Ba da Shawara kan Tsaron Ƙasa, Ismail Garba, ya yi alƙawarin bayar da amsa amma bai yi hakan ba har bayan kwanaki da dama.

Mataimakin Manajan Binciken Kasuwa na JetHQ, Marinell Nuevo, ya tabbatar da cewa jirgin “yana nan a kasuwa” amma ya tura karin tambayoyi zuwa Barringer.

Daga baya Barringer ya bayyana cewa kamfanin ba zai bayyana wasu bayanai fiye da kasancewar jirgin a kasuwa ba, yana mai cewa irin wannan bayani na sirri ne.

“Ba ma bayar da irin wadannan bayanan ga kowa sai ga mamallakin jirgin kai tsaye. Ana ɗaukar wannan bayani a matsayin sirri. Ina fatan za ku fahimta. Abin kawai da za mu iya bayarwa shi ne cewa jirgin yana nan a kasuwa,” in ji Barringer.

Kafin a cire shi daga jerin sayarwa, bayanai sun nuna cewa an yi wa jirgin gyare-gyare a watan Yuli 2024, ciki har da gyaran kujerun ajin farko, sauya kafet na cikin jirgi da sauran kananan gyare-gyare.

A cewar aircraftcostcalculator.com, jirgin Boeing 737 BBJ da aka taɓa amfani da shi darajarsa a kasuwa ta kai kusan $56m, kwatankwacin Naira sama da Naira biliyan 82.

An sayi jirgin a shekarar 2005 a kan $43m a zamanin tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo, kuma ya kasance wani jerin jiragen Fadar Shugaban Ƙasa.

A watan Yuli 2025, gwamnatin Tinubu ta sanar da shirin sayar da jirgin a matsayin wani ɓangare na dabarar rage kashe kuɗi da daidaita yawan jiragen, a yayin da jama’a ke ƙara sa ido kan yadda gwamnati ke kashe kuɗade.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shettima Ya Taya Sarkin Gumel Murna Tare da Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Bunkasa Bangaren Noma
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • NAJERIYA A YAU: Abun Da Masu Ruwa Da Tsaki Ke Yi Na Dakile Laifuka A Wurin Matasa
  • Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
  • Isra’ila Ta Hana Motocin Agaji 6000 Shiga Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta
  • Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro