Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta bullo da tsarin da kowanne maniyyaci zai san masaukinsa a kasa mai tsarki tun daga nan gida najeriya.

Shugaban hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a shalkwatar hukumar dake Dutse.

Yana mai cewar, wannan shi ne karon farko da hukumar ta bullo da tsarin domin maniyyaci ya san masaukinsa a nan gida kafin zuwa kasa mai tsarki.

Game da batun kudade kuwa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma kaddamar da kwamitin canjin kudaden guzuri na maniyyata domin samun saukin canji yayin aikin Hajjin.

Ya ce an kafa kwamitin ne domin  bibiyar maniyyata kan canjin kudin guzuri, kasancewar wasu batagari na damfarar mahajjata a kasa mai tsarki wajen canjin kudade daga Dala zuwa Riyal.

Ya kara da cewar, hukumar ta turawa hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON fiye da naira miliyan dubu shida da miliyan dari uku da talatin da daya (6,331,000,000) a matsayin kudaden maniyyatan aikin hajjin bana.

Ya ce jihar Jigawa ce ta farko wajen biyan kudaden aikin hajjin bana ga hukumar aikin hajji ta kasa.

Ahmed Umar Labbo ya kara da cewar Gwamnatin jihar ta baiwa hukumar rancen naira miliyan dubu uku da miliyan dari uku da sittin (3,360,000,000) da ta yi amfani da shi wajen sayen kujerun aikin hajjin bana daga hukumar aikin hajji ta kasa.

Umar Labbo, ya ce sun cimma kaso 95 bisa 100 na aikin bada biza ga maniyyata.

Babban Daraktan ya shedawa mahalarta taron cewar hukumar ta kammala duk wani shiri na fara jigilar maniyatan  wanda za a fara jigilar alhazan Najeriya a ranar tara ga watan Mayu.

Kazalika, wakilan hukumomin tsaro sun yi bayani akan shirye shiryen da suke yi domin tunkarar aikin hajjin bana

Ya kuma yi kira ga maniyyatan jihar, da su ci gaba da halartar cibiyoyin bita domin samun ilimin da za su gudanar da aikin hajji cikin sauki.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi

Daga Bashir Meyere

Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da bukatar Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, na neman rancen Naira Tiriliyan 1.15 domin cike gibin kasafin kudin shekarar 2025.

Amincewar ta biyo bayan gabatar da rahoton kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da lamuran bashi na cikin gida da na waje.

Yayin da yake gabatar da rahoton, shugaban kwamitin, Sanata Aliyu Magatakarda Wamako, wanda mataimakinsa Sanata Haruna Manu ya wakilta, ya bayyana cewa kasafin kudin shekarar 2025 na Naira tiriliyan 59.99 da Majalisar ta amince da shi, ya karu da Naira tiriliyan 5.25 idan aka kwatanta da Naira tiriliyan 54.74 da gwamnatin tarayya ta fara gabatarwa.

Ya ce an riga an amince da Naira tiriliyan 12.95 a cikin kasafin, wanda hakan ya bar gibin  Naira tiriliyan 1.147, abin da ya haifar da bukatar wannan shirin neman rance.

Kwamitin ya bai wa Majalisar shawarar  amincewa da rancen cikin gida na Naira tiriliyan 1.15 domin cike gibin da ya samo asali daga karin kudin kasafin.

Kwamitin ya kuma bukaci Ministar Kudi  da Ofishin Kula da Lamuran Bashi su tabbatar da cewa an aiwatar da rancen cikin tsari, tare da bin ka’idojin gaskiya,  da sharuɗɗan da suka dace.

Majalisar Dattawa ta kuma umurci kwamitinta mai kula da bashin cikin gida da na waje da ya rika sa ido kan yadda za a aiwatar da amfani da kudin da aka ciwo bashi.

Haka kuma, Ministar Kudi za ta rika mika rahoton kowane watanni uku kan halin da ake ciki, da amfani da kudaden, da yadda ake biyan basussuka, yayin da za a kai duk wani rahoton sabawa tsarin  ga Majalisar Dattawa domin daukar matakin doka da ya dace.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan bindiga suka kashe banga 16 suka sace mutane 42 a Neja
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yanga 16 sun sace mutane 42 a Neja
  • NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026
  • HOTUNA: NDLEA ta ƙone tan dubu 52 na miyagun ƙwayoyi a Zariya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji A Najeriya
  • MURIC ta buƙaci Tinubu ya sauke Amupitan daga shugabancin INEC
  • Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa
  • Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi
  • Gwamnatin Jigawa Ta Himmatu Wajen Inganta Harkokin Kiwon Lafiya a Jihar
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki