Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta bullo da tsarin da kowanne maniyyaci zai san masaukinsa a kasa mai tsarki tun daga nan gida najeriya.

Shugaban hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a shalkwatar hukumar dake Dutse.

Yana mai cewar, wannan shi ne karon farko da hukumar ta bullo da tsarin domin maniyyaci ya san masaukinsa a nan gida kafin zuwa kasa mai tsarki.

Game da batun kudade kuwa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma kaddamar da kwamitin canjin kudaden guzuri na maniyyata domin samun saukin canji yayin aikin Hajjin.

Ya ce an kafa kwamitin ne domin  bibiyar maniyyata kan canjin kudin guzuri, kasancewar wasu batagari na damfarar mahajjata a kasa mai tsarki wajen canjin kudade daga Dala zuwa Riyal.

Ya kara da cewar, hukumar ta turawa hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON fiye da naira miliyan dubu shida da miliyan dari uku da talatin da daya (6,331,000,000) a matsayin kudaden maniyyatan aikin hajjin bana.

Ya ce jihar Jigawa ce ta farko wajen biyan kudaden aikin hajjin bana ga hukumar aikin hajji ta kasa.

Ahmed Umar Labbo ya kara da cewar Gwamnatin jihar ta baiwa hukumar rancen naira miliyan dubu uku da miliyan dari uku da sittin (3,360,000,000) da ta yi amfani da shi wajen sayen kujerun aikin hajjin bana daga hukumar aikin hajji ta kasa.

Umar Labbo, ya ce sun cimma kaso 95 bisa 100 na aikin bada biza ga maniyyata.

Babban Daraktan ya shedawa mahalarta taron cewar hukumar ta kammala duk wani shiri na fara jigilar maniyatan  wanda za a fara jigilar alhazan Najeriya a ranar tara ga watan Mayu.

Kazalika, wakilan hukumomin tsaro sun yi bayani akan shirye shiryen da suke yi domin tunkarar aikin hajjin bana

Ya kuma yi kira ga maniyyatan jihar, da su ci gaba da halartar cibiyoyin bita domin samun ilimin da za su gudanar da aikin hajji cikin sauki.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi

Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun gano wurin da ’yan bindiga suka tsugunar da ɗalibai mata 25 da suka sace daga makarantar kwana ta Maga da ke Jihar Kebbi.

A wani taron manema labarai a Birnin Kebbi, Matawalle ya ce a halin yanzu an tsananta aikin leƙen asiri da tsare-tsare, tare da bayyana cewa ba da jimawa ba za a kuɓutar da ɗaliban cikin nasara, idan komai ya tafi yadda ake so.

An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF

Ya nemi goyon bayan al’umma, yana mai cewa, “Haɗin kan jama’a na da matuƙar muhimmanci domin ganin an kammala wannan aiki lafiya lau, tare da dawo da yaran cikin iyayensu ba tare da wata matsala ba.”

A ranar Litinin da ta gabata ne ’yan bindiga suka kai mummunan hari makarantar ta Maga, inda suka yi awon gaba da ɗalibai mata 25, lamarin da ya tayar da hankalin al’umma musamman ma iyayen yaran.

Ministan ya ce tun bayan faruwar lamarin, Gwamnatin Tarayya ta tura ƙarin jami’an tsaro, ciki har da rundunar sojin sama da ta ƙasa, waɗanda ke aiki tare domin gano hanyar shiga ba tare da hallaka ko jikkata ɗaliban ba.

Ya ce, “Mun gano wurin da aka tsare yaran kuma da Yardar Allah za mu ceto su nan ba da jimawa ba. A yanzu haka muna a matakin ɗaukar tsattsauran mataki cikin hikima, domin tabbatar da cewa babu wata illa da za ta same su.”

“Ina kira ga al’ummar Kebbi da su ci gaba da haƙuri da kuma bayar da haɗin kai ga jami’an tsaro. A irin wannan lamari, bayanan sirri daga jama’a na da matuƙar muhimmanci,” in ji shi.

Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi

A bayan nan ne Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarci Ƙaramin Ministan Tsaron da ya koma Jihar Kebbi da aiki sakamakon sace ɗaliban da wasu ’yan bindiga suka yi a jihar.

Tinubu ya umurci Matawalle, wanda tsohon Gwamnan Jihar Zamfara ne, da ya zauna a Kebbi domin sa ido kan dukkan matakan tsaro da ake ɗauka domin kuɓutar da ɗaliban da aka sace.

A cewar mai magana da yawun fadar shugaban ƙasa, Bayo Onanuga wanda ya bayyana umarnin a cikin wata sanarwa da yammacin Alhamis, ana sa ran Matawalle zai isa Birnin Kebbi da safiyar Juma’a.

“Yana da ƙwarewa sosai wajen fuskantar ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane a lokacin da yake gwamnan Jihar Zamfara daga 2019 zuwa 2023,” in ji sanarwar.

“A ranar 26 ga watan Fabrairu, 2021, ’yan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai mata 279 masu shekaru tsakanin 10 da 17 a makarantar kwana ta GGSSS Jangebe, Jihar Zamfara. ’Yan bindigar sun saki dukkan waɗanda suka yi garkuwar da su a ranar 2 ga watan Maris, 2021.”

Aminiya ta ruwaito cewa, shi ma dai Shugaba Tinubu ya ɗage tafiyarsa da aka tsara zuwa Johannesburg, Afirka ta Kudu, da Luanda a ƙasar Angola, domin ci gaba da samun rahotannin tsaro kan satar ɗaliban na Kebbi da kuma harin da aka kai wa masu ibada a cocin Eruku da ke Jihar Kwara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi
  • Najeriya Ta Cimma Sabon Tsarin Hadin Gwiwa Kan Sha’anin Tsaro da Amurka
  • Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kwara Ta Sanar da Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajjin 2026
  • Iran ta sake tir da sabon kudurin da Hukumar (IAEA)
  • Iran: HKI Na Faskantar Mummunan Aikin Leken Asiri Daga Kasar
  • An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi
  • H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a Jigawa
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Za Ta Mayar Da Rarar Kudi Ga Maniyyatan 2026