Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta bullo da tsarin da kowanne maniyyaci zai san masaukinsa a kasa mai tsarki tun daga nan gida najeriya.

Shugaban hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a shalkwatar hukumar dake Dutse.

Yana mai cewar, wannan shi ne karon farko da hukumar ta bullo da tsarin domin maniyyaci ya san masaukinsa a nan gida kafin zuwa kasa mai tsarki.

Game da batun kudade kuwa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma kaddamar da kwamitin canjin kudaden guzuri na maniyyata domin samun saukin canji yayin aikin Hajjin.

Ya ce an kafa kwamitin ne domin  bibiyar maniyyata kan canjin kudin guzuri, kasancewar wasu batagari na damfarar mahajjata a kasa mai tsarki wajen canjin kudade daga Dala zuwa Riyal.

Ya kara da cewar, hukumar ta turawa hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON fiye da naira miliyan dubu shida da miliyan dari uku da talatin da daya (6,331,000,000) a matsayin kudaden maniyyatan aikin hajjin bana.

Ya ce jihar Jigawa ce ta farko wajen biyan kudaden aikin hajjin bana ga hukumar aikin hajji ta kasa.

Ahmed Umar Labbo ya kara da cewar Gwamnatin jihar ta baiwa hukumar rancen naira miliyan dubu uku da miliyan dari uku da sittin (3,360,000,000) da ta yi amfani da shi wajen sayen kujerun aikin hajjin bana daga hukumar aikin hajji ta kasa.

Umar Labbo, ya ce sun cimma kaso 95 bisa 100 na aikin bada biza ga maniyyata.

Babban Daraktan ya shedawa mahalarta taron cewar hukumar ta kammala duk wani shiri na fara jigilar maniyatan  wanda za a fara jigilar alhazan Najeriya a ranar tara ga watan Mayu.

Kazalika, wakilan hukumomin tsaro sun yi bayani akan shirye shiryen da suke yi domin tunkarar aikin hajjin bana

Ya kuma yi kira ga maniyyatan jihar, da su ci gaba da halartar cibiyoyin bita domin samun ilimin da za su gudanar da aikin hajji cikin sauki.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu”

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Dangantaka na ƙara rincaɓewa tsakanin masu shirya finafinai Kannywood da Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano, wacce daya daga cikin jaruman fina-finan Kannywood Abba El-Mustapha, ke jagoranta.

A baya-bayan nan, hukumar ta dakatar da fina-finai masu dogon zango guda 22, bayan saɓaninta da wasu masu shirya fina-finai, inda take zargin cewa fina-finansu sun ƙetare iyaka.

Sai dai masu shirya fina-finan sun bayyana cewa sam hukumar ba ta da hurumin dakatar da waɗannan finafinai.

NAJERIYA A YAU: Yadda Za Ku Kula Da Lafiyar Jikinku DAGA LARABA: Tasirin Mulkin Karɓa-Karɓa A Najeriya

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan rigimar da ta balle tsakanin hukumar da masu shirya finafinai masu dogon zango.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajjin 2025: Kashi 79 na maniyyatan Najeriya sun isa Saudiyya – NAHCON
  • Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77 Na Mahajjatan Nijeriya Zuwa Saudiyya 
  • Jigajigan Jihar Kebbi Sun Bukaci Hadin Kan ‘Ya’yan Jam’iyyar APC
  • DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu”
  • Maniyatan Jigawa 550 Sun Isa Kasa Mai Tsaki Don Aikin Hajjin Bana
  • An kama ɗan bindiga a hanyar zuwa aikin Hajji a Sakkwato
  • DSS ta kama ɗan bindiga a cikin maniyyata aikin Hajji a Sakkwato
  • Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Tsaro
  • Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200
  • Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya ba su kyautar Riyal 200