Jigawa Ta Bude Sabon Babi: Maniyyata Za Su San Masaukansu Tun Daga Gida Najeriya
Published: 25th, April 2025 GMT
Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta bullo da tsarin da kowanne maniyyaci zai san masaukinsa a kasa mai tsarki tun daga nan gida najeriya.
Shugaban hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a shalkwatar hukumar dake Dutse.
Yana mai cewar, wannan shi ne karon farko da hukumar ta bullo da tsarin domin maniyyaci ya san masaukinsa a nan gida kafin zuwa kasa mai tsarki.
Game da batun kudade kuwa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma kaddamar da kwamitin canjin kudaden guzuri na maniyyata domin samun saukin canji yayin aikin Hajjin.
Ya ce an kafa kwamitin ne domin bibiyar maniyyata kan canjin kudin guzuri, kasancewar wasu batagari na damfarar mahajjata a kasa mai tsarki wajen canjin kudade daga Dala zuwa Riyal.
Ya kara da cewar, hukumar ta turawa hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON fiye da naira miliyan dubu shida da miliyan dari uku da talatin da daya (6,331,000,000) a matsayin kudaden maniyyatan aikin hajjin bana.
Ya ce jihar Jigawa ce ta farko wajen biyan kudaden aikin hajjin bana ga hukumar aikin hajji ta kasa.
Ahmed Umar Labbo ya kara da cewar Gwamnatin jihar ta baiwa hukumar rancen naira miliyan dubu uku da miliyan dari uku da sittin (3,360,000,000) da ta yi amfani da shi wajen sayen kujerun aikin hajjin bana daga hukumar aikin hajji ta kasa.
Umar Labbo, ya ce sun cimma kaso 95 bisa 100 na aikin bada biza ga maniyyata.
Babban Daraktan ya shedawa mahalarta taron cewar hukumar ta kammala duk wani shiri na fara jigilar maniyatan wanda za a fara jigilar alhazan Najeriya a ranar tara ga watan Mayu.
Kazalika, wakilan hukumomin tsaro sun yi bayani akan shirye shiryen da suke yi domin tunkarar aikin hajjin bana
Ya kuma yi kira ga maniyyatan jihar, da su ci gaba da halartar cibiyoyin bita domin samun ilimin da za su gudanar da aikin hajji cikin sauki.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Duniyarmu A Yau: Ranar 40 Ta Imam Hussain (a) A Bana
Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na duniyarmu a uau shiri wanda yake kawo mako labarai masu muhimmanci a makon da ya gabata, wadanda suka shafi siyasa tattalin arziki zamantakrwa , tsaro da sauransu. Sannan mu yi masu Karin bayani daga karshe mu ji ra’ayin masana dangane da su da fatan masu saurarozasu kasance tare da mu a cikin shirimmu nay au.
////…Madallah, masu sauraro shirimmu nay au zai dubi “ranar 40 na Imam Hussain(a) wanda ya fado a ranakun Alhamis ko jumman da suka gabata, a nan Iran da kuma Iraki, kowa da yadda suke yi lissan watan Safar a wajensu. Ranar 40 na Imam Hussain (a) ita ce ranar 20 ga watan Safar na ko wace shekara tun bayan shahadar Imam Husain (a) a ranar 10 ga watan Muharram shekara ta 61 bayan hijira. Wato daga 10 ga watan muhaharran na ko wace shekara zuwa 20 ga watan Safar na shekarar ne yace cika kwanaki 40 daga shahadarsa.
Shadar Imam Hussain (a) wanda hadisan manzon All…(S) da dama sun bayyana aukuwarsa da kuma abinda musulmi zasu yi idan haka ya auku. Muna da hadisai wadanda suka tabbatar da cewa manzon All..(s) ya yi kukan shahadar Hussain (a) a ranar da aka haifeshi, da aka tambayeshi sai yace al-ummata zasu kasheshi.
A waniahadisi dana Umma salamamatar manzon All..(s) tana cewa wata rana manzon All..yana kuka sai ta tambaye shiabinda ya sa yake kuka, sai yace yanzu din nan Jibrilu ya tashi daga waje ne ina wata da dana Hussai sai yace mani kanason ce ne, sai yace ina sonsa, sai yace masa amma al-ummanka zasu kashe a wani wurida aki kira karbala, sai ya mike ya debomani kasarya bani a hannu na, sai ya nuna mata kasar. Shi yasa yake kuka, sannan y ace mata ta ajiye wannan kasar a duk lokacinda ta ya zama jini to an kashe Husain.
A wani hadisin manzon All..(s) yana Magana kan hussain(a). ya sanshi bakin ciki saboda kasansa alamane na Imani, yana cewa: Lalle, kissan Hussain yana da kuna a cikin zuciyar mumini, ba zai dushe ba har’abada.
A wani hadisin yana cewa: Hussain daga gareni yaki, ni kuma daga gareshi nake, All..ya so wanke yake son Hussaini, Hussain jika ne daga jikokin (annabawa).
Da kuma wasu hadisai da dama. Kafin haka yana daga cikin wadanda aka tsarkaka a aytar Tathir, yana daga cikin ayar Mubahala, yana daga cikin wadanda All..a cikin alkur’ani mai girma ya wajabta sonsu, kuma hakan shi ne, ladar annabcin manzon All..(s), yana daga cikin wadanda aka saukar da suratu Hal’ata a kansu.
Ayoyin alkur’ani da dama sun sauka suna yabonsu, wato iyalan gidan manzon All..(s). Rayuwar Imam Hussain da dukka Alhlu baitin manzon All…(s) yana da dangantaka da makoman Al-ummar manzon All..(s). Kuma iyalan gidansa sun zama cikin jirrabawar da All…ya jarribi wannan al-ummar da su don ya ga abinda al-ummar zata ya sau.
Lalacewa al-ummar manzon All..(s) ya kai ga, bayan da aka kwace iko daga hannun wasiyyinsa na farko ko mahaifin sauran wasiyyan, al-umma ta kasa dawo mata da hakkinsa, har zuwa lokacinda, mutanen suka yi tawaye suka kashe khalifa na uku saboda zaluncin da danginsa sukewa al-ummar, sannan bayan sun kashe shi, sun tilasta masa ya zama shugabansu, yi ki amincewa, har sai ya ga cewa abinda bai karba ba to zai ga abinda yafi halin da ake ciki muni, sannan suka taimaka masa ya murkushe boren da aka yi masa na farko, amma bayan yakin siffin da Nehrawan, sun kasa taimaka masa, y agama da mu’awiya har sai da abubu suka fita hannu, bayan shahadarsa dans ana farko ya karbi jagoranci, amma suka ki taimaka masa, har aka tilasta masa yin sulhu da Mu’awiya dan Abusufyan.
A nan ne suka fara gane kurakuransu, amma lokaci ya kure, wasu sun dawo wajen imam Hassan kafi yayi shahada, sai suka ce masa mun yi kuskure da bamu taimaka maka ba. Sai yace ai kuma kunyi lattin. Shi ma ya yi shahada, a lokacinda al-amarin ya kai Imam Hussain(a), lalacewar ta kai ga abinda zai ya farkar da mutanen daga bacci mai zurfi da suka daga kare addinin All..ya bada jininsa, sai an kashe shi a daga kansa an kashi ana yawo da shi gari gari.
A ce wannan bakhawarije ne wan ya ki bai’a ga yazid, amma daga karshe su gano cewa ai jikan manzon All..(a) ne dan Fatimah dayar manzon All…wanda All..ya daukaka larabawa da shi, ya aiko da addinin karshe kuma yayi alkawalin wannan addinin sai ya mamaye duniya, kuma shi ne addinin gaskiya wanda All..ya yarda ya zama addini.
Shin wannan shi ne sakamakon da kuma ladar da zaku yiwa wannan annabin, ku yanka kansa kuna yawo da shi a cikin garuruwanku?.
Da wannan Imam Hussain (a) ya farkar da zukata wadanda basu mutuba, limamai da suka zo mayansa suka karfafa batun makokin Imam hussain da nufin jaddada makakin a cikin zukatan musulmi, mai yuwa wanda zai farka ya farka. Kuma a duk tsawon tarihin musulunci an samun masu farkawa saboda raya al-amarin Imam Hussain(a) raya tasuaa da Ashoora. Raya 40 na Imam Hussain.
A hidisi Imam Sadika(a) yana cewa : Ku ziyarci junan ku, ku zauna ku tattauna dangane da Al-Amarimmi (wato shugabanci da jagoranci) ku raya al-amarimmu wao Ahlul baiti(a).
Imam Rida (a) yana cewa: Ya kai dan Shubaib, idan zaka yi kuka kayi kokan Hussain dan Aliyu dan Abitalib (a) Al-Hussain, lalle shi an yankashi kamar yadda ake yanka rago.
Don haka raya shahadar Imam Husain(a) ya hada da ranakun tasu’a da Ashoora da 40 da kuma ko yaushe a duk lokacinda suka aka sami danar yin haka. Dukkaninsu a kawai Hadisan manzon All..(a) da kuma lilamamai masu tsarki (a).
Sannan a duk tsawon tarihin musulunci azzaluman sarakunan sun yi iya yinsu yinsu, don hana Mabiya iyalan gidan manzon All..(a) raya wadannan kwanaki, ko kuma ziyartar kabarin Imam Hussain (a). wasu sun rusa hubbaren da akan kabarinsa, suka maida wurin gona, wasu sarakunan sun yanka kafa da hannayen duk wanda ya yi kokarin ziyarar kabarin Imam Hussain(a).
Amma duk kokarinsu ya tashi a banza, don ba wanda ya isa ya hana abinda All..ya kaddara sai ya faru.
Don haka raya wadannan ranakun sun bunkasa, sosai a wannan zamanin ha rya kaiga miliyoyin mutanene daga ciki da wajen Iraki suke ziyartar kabarin Imam Hussain (a).
Marigayi Imam Khomaini(q) wanda ya kafa JMI yana cewa: duk abinda muka samu daga Ashora ne, yana cewa duk rana ashoora ce kuma duk kasa karbala ce.
Don hala a wannan zamanin, musamman bayan nasarar da aka samu a JMI na kafa daula wacce take bin iyalan gidan manzon All..(a) a Iran, 40 na Imam Hussain (a) ya bunkasa, ya kuma fi daukar bangaren siyasa a kan sauran bangarorin kamar na samun kusanci ga All..T, saboda mafi yawan kasashen musulmi suna karkashin azzaluman sarakuna ko kuma karkashin iko kafirai. Wanda suke azbatar da su.
Don haka lamarin Imam Hussain (a) ya zama ramzi ne na samun yenci ya yakar azzalumai ko kafirai wadanda suke mamaye da kasashen musulmi da kuma
Al-amarin Imam Hussain(a) ya zama a wannan zamani lokaci ne na nuna karfin musulmi da hadin kansa, musamman tsakanin mabiya mazhabar Ahlulbaiti (a). Musamman kuma tsakanin Iran da Iraki, wadanda sune lasashen da shia suka fi rinjaye a duniya a cikinsu, hatta gwamnatocinsu ba na shia ne.
A Iran a shekara ta 1979 Imam Khomaini (a) daya daga cikin manya-manyan malaman shia a lokacin ya sami nasarar korar sarki sha daga kan kujerar sarautar kasar ya kuma kafa JMI wanda tsarin mukinsa da dukka al-amuransa suna tafiya karkashin tsarin mulki na mazhabar shia ne. da kuma Iraki inda mafi yawan mutanen kasar Shia ne kuma yana yana dauke da hubbarin limamai 6 daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All…(s). kuma birnin Najaf wanda na ne kabarin limamai na farko da cikin limaman, wato Aliyu dan Abitalib (a) yake.
Don haka iraki tana daga cikin cibiyoyin ilmi na mazhabar tun karni na 4 ko 5 hijiriyya tsakanin Najaf da Karbala. Sannan birnin Qom a kasar Iran na daga cikin cibiyoyin bada ilmi na mazhabar Iyalan gidan manzon All..(s) tun da danewa sannan hubbaren limami na 8 daga cikin liamaman masu tsarki yana birnin Mashhad a na arewa maso gabacin kasar.
Ganin yadda kasashen yamma suke adawa da samuwar JMI a Iran shekaru kimani 47 da suka gabata, ga kuma yadda cikinci ke yaduwa a duniya, kaashen yamma suna jin tsoro matuka kan cewa daga wadannan kasashen biyu, iran da iraki suna iya zaman masomin tawaye babban nan gaba ga turawan da kuma sauran kasashen musulmi a yankin da kuma sauran kasashen duniya.
Har’ila yau kasashen yamma suna jin tsoron daga cikin wadan nan kasashe biyu ko kuma daga Iran musulmi suna iya dogaro da ita su kauda HKI daga yankin wacce turawan ingila suka kafata bayan sun sami nasarar kada daular Uthmaniya ta musulmi shekaru 76 da suka gabata. Wanda kuma yake nuna raguwar karfin kafirai a kan musulmin yankin. Wanda daga karshe zai bude kofar fitar kasashen duniya da dama daga mulkin mallakar da suke masu tun daruruwan shekaru da suka gabata.
Daga nan muna iya cewa 40 na Imam Hussain (a) ya tashi daga al-amarin na addinin da kuma al-ada a cikin mabiya iyalan gidan manzon All..(s) ya zama wani al-amari wanda yake ingiza shia a ko ina suke a duniya su yi fada da zalunci. Su nuna jarunta wajen yakasar azzaluman sarakuna a cikin musulmi ko kuma sauran kafiran duniya.
Al-amarin Imam Hussain ya zama sunan da dukka azzalumai a ko ina suke a duniya, idan sun ji sunansa sai hantarsu ta kada.
Sannan daga karshe wannan halin zai ci gaba har zuwa lokacinda, kamar yadda musulmi gaba daya suka yi imanin cewa limami na 12 (a) zai zo ya ci duniyar da yaki ya kuma shimfida a dalci bayan cikarta da zalunci kamar yadda manzon All..(s) ya fada a cikin hadisai mustafida. Wato da yawa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Larijani: Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wanda Ya Kai Mata Hari August 15, 2025 HRW; Kai Hari Kan Gidan Yarin Evin Na Iran Laifin Yaki Ne August 15, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Wani Mummunan Hari Kan Gaza August 15, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza August 15, 2025 Gwamnatin Mali Ta Bankado Wata Makarkashiyar Janyo Hargitsi A Kasar Tare Da Wargaza Shi August 15, 2025 Iran: Suna Bukatar Kawo Karshen Makaman Nukiliya Da Kuma Furuci Maras Daɗin Ji August 15, 2025 Kungiyar Ansarullahi Ta Kasar Yemen Ya Ce; Yahudawan Sahayoniyya Suna Yakar Al’ummar Falasdinu Duka Ne August 15, 2025 Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Koka Kan Hana Shigar Da Kayayyakin Jin Kai Yankin Gaza August 15, 2025 Laifukan Cin Zarafi Musamman Kisha Kiyashi A Kasar Siyasa Ya Doshi Laifukan Yaki August 15, 2025 Kungiyar Ba Da Agaji Ta Sanar Da Yadda Cutar Kwalara Take Lashe Rayukan Mutane A Kasar Sudan August 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci