Leadership News Hausa:
2025-07-05@22:17:37 GMT

An Sako Malamin Kiristan Cocin Katolika Da Aka Sace A Kaduna

Published: 25th, April 2025 GMT

An Sako Malamin Kiristan Cocin Katolika Da Aka Sace A Kaduna

Farfesa Ibrahim Amos, wani Malamin cocin Katolika, ya samu ‘yanci daga hannun masu garkuwa da mutane a Jihar Kaduna, bayan an sace shi a ranar Alhamis, 24 ga Afrilu, 2025, daga gidansa a St. Gerald Quasi Parish, Kurmin Risga, ƙaramar hukumar Kauru.

Wani shugaba a ɗariƙar dake Kafanchan, Rev. Fr. Jacob Shanet, ya tabbatar da sakin farfesan a cikin wata sanarwa da aka mikawa manema labarai.

Ya bayyana cewa Farfesa Amos ya dawo lafiya jiya Alhamis ɗin da aka sace shi, amma bai bayyana yadda aka sake shi ba ko sun biya kuɗin fansa ba.

Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna  2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna

Rev. Fr. Shanet ya gode wa jama’ar alheri, da ƙungiyoyin addini, da jami’an tsaro, da sauran masu ƙoƙarin ganin an sake shi. Ya jaddada cewa, goyon bayan da aka samu daga kowanne ɓangare ya tabbatar da cewa ba su kaɗai ke ƙoƙarin tabbatar da darajar rayuwar dan Adam ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani

Sheikh Na’in Kasem shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ya bayyana cewa kungiyar bata bukatar Izini don kare kasar Lebanon daga makiyanta. Yama fadar haka ne ga wanda suka cika kunnen duniya kan cewa dole ne kungiyar ta mika makamanta ga gwamnatin kasar.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim ya nakalto Sheikh Kasim yana fada a wani jawabin da ya gabatar a ranakun Ashoora na Imam Hussain (a) ta kafar Bidiyo. Ya kuma kara da cewa wadanda suke maganar kungiyar Hizbullah ta mika makamanta ga gwamnatinsa kasar, ya fiye masu sauki su fadawa yan mamaya su fice daga kasar Lebanon su kuma dakatar da hare-haren ta’addancin da suke kawo mata.

Ya kara jaddada cewa kungiyarsa zata ci gaba da rike makamanta sannan bata bukatar izini daga wani don kare-kasar Lebanon daga makiyanta.

Malaman ya kara da cewa, wani mai hankali ne zai amince ya mika makamansa a dai dai lokacinda mikiyan kasar Lebanon suna ci gaba da kawo hare-hare kan  kasar a ko wace rana. Maimakon su yi allawadai da mai shisgigi sai suka sa idanso a kan makaman hizbulla.

Yace idan wasu a kasar Lebanon sun zami mika kai ga HKI da Amurka to wannan zaminsa ne, amma mu ba masu mika kai ga makiyammu ne ba. Shi’arimmu shi ne {bama daukar kaskanci}.

Ya ce kun yi kuskure da kuka dogara da karfin wasu don takurawa masu gwagwarmaya. Masu gwagwarmaya basa jin tsoron makiya. Ya ce manufarmu ita ce yantar da kasa daga hannun makiya itace manufarmu.

Ya kammala da cewa makiyarmu it ace HKI, dole ne ta fice daga kasar Lebanon, kuma gwagwarmaya ita ce hanya tilo ta korar yan mamaya daga kasarmu. Idan kuma wani yana ganin akwai wata hanya korar makiya daga kasarmu a shirye muke mu shiga tataunawa da shi, ya gamsar damu a kan shirin nasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Ana raɗe-raɗin Sanata Lamiɗo zai fice daga APC zuwa ADC
  • Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
  • Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jiran Amsar Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
  • SON Ta Bada Shaidar Ingancin Kayayyaki Ga Wasu Kamfanoni A Kaduna
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jirin Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram