Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-03@13:35:53 GMT

Gwamnatin Jihar Sakkwato Na Maraba Da Masu Zuba Jari

Published: 13th, February 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Sakkwato Na Maraba Da Masu Zuba Jari

Gwamnatin jihar Sokoto ta ce tana kokarin samar da sauki da kuma tsarin zuba jari mai inganci wanda zai iya karfafa gwiwar masu zuba jari daga kasashen waje da na cikin gida zuwa jihar.

 

Wakilin Gwamnatin jiha kuma shugaban karamar hukumar Wamako Alh. Umar Ahmad Dundaye ya bayyana haka ne a wajen rabon magunguna da kamfanin siminti na BUA ke gabatarwa a kowace shekara ga asibitocin al’umma goma sha shida da ke yankin.

 

Ya ce gwamnatin jihar Sokoto tana karfafa duk masu zuba jari da ke da alaka kai tsaye ga ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin jihar.

 

Ya ce gudunmawar BUA a fannin kiwon lafiya na jihar na daya daga cikin alfanun da jarin jihar ke samu.

 

Shugaban ya kara da cewa, a wani bangare na ayyukan da ya rataya a wuyan kamfanin, kamfanin yana kara habaka dimbin albarkatu wajen bunkasa al’ummomin da suka karbi bakuncinsa a karkashin karamar hukumar Wamako.

 

A nasa jawabin, Manajan Daraktan kamfanin simintin Alh. Yusuf Binji ya ce tallafawa al’ummomin da suka karbi bakuncinsu yana da matukar muhimmanci a wani yunkuri na kara kima ga zamantakewa da zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin jama’ar yankin.

 

Nasir Malali/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Za Ku Hada Fab Biskit
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida