Kungiyar Shugabannin Arewa (NEF) ta zargi Shugaba Bola Tinubu da nadin mukaman gwamnati ba tare da daidaito tsakanin yankunan Nijeriya ba, wanda ta ce yana fifita yankin Kudu maso Yamma a kan sauran yankuna shida na kasar.

Mai magana da yawun kungiyar, Farfesa Abubakar Jiddere, a cikin wata sanarwa a yau Juma’a a Abuja, ya bayyana cewa nadin da aka yi sun karkata ne wajen goyon bayan Kudu maso Yamma, yayin da sauran yankunan suka samu kadan ko kuma aka danne su.

Gazawar Gwamnatin Tinubu Ce Ke Haddasa Zubar Da Jini A Filato – Ƙungiyar Dattawan Arewa Rurum Ya Shawarci Mafarautan Arewa Da Su Daina Zuwa Kudu Farauta 

NEF ta bayyana cewa wannan lamari ya sabawa tsarin hadin kan kasa, sannan ya saba wa tanadin kundin tsarin mulkin Nijeriya, wanda a sashi na 2, da sashi na 14(3), ya tanadi cewa a kiyaye manufar adalci a nadin mukamai da rarraba albarkatun kasa.

Kungiyar ta kuma yi tir da sabon kwamitin kidayar jama’a na kasa, wanda ta ce yana da fifiko sosai a Kudu maso Yamma, wanda ke nuna rashin daukar wasu yankuna da muhimmanci. NEF ta yi kira da a sake duba wannan kwamitin domin tabbatar da daidaito tsakanin dukkanin yankunan kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Professor Abubakar Jiddere

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu

Hukumomin ’yan sandan Najeriya tare da haɗin gwiwar wasu hukumomin tsaro sun samu gagarumar nasara a ƙoƙarin da suke na daƙile munanan laifuka a ƙasar.

Na baya-bayan nan dai shi ne ceto mutanen da aka sace, da kashe wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da kuma ƙwato manyan bindigogi da alburusai a jihohin Delta da Katsina.

Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce a jihar Katsina an samu gagarumar nasara a ranar 8 ga watan Yunin 2025, inda haɗin gwiwar JTF da suka haɗa da jami’an ’yan sanda da sauran jami’an tsaro suka daƙile wani yunƙurin yin garkuwa da mutane a hanyar ƙauyen Danmusa  zuwa  Mara Dangeza a ƙaramar hukumar Danmusa.

Adejobi ya ce hakan na iya yiwuwa ne ta hanyar shigar da wasu gungun ’yan bindiga da suka yi yunƙurin guduwa da waɗanda aka yi garkuwa da su a wani artabu da ya kai ga ceto mutum 11.

Nasarar da aka samu yankin Kudu maso Kudu

A halin da ake ciki kuma, a yankin Kudu maso Kudu, Jihar Delta, hukumar ’yan sanda ta kama wani Abubakar Hassan, wanda babban wanda ake zargi da aikata laifin satar mutane ne a tsakanin jihohin Delta da Ribas da Imo, da Enugu.

Jami’an da ke da alaƙa da samun nasarar sun yi hakan ne yayin da suke aiki da sahihan bayanai.

A yayin da ake yi masa tambayoyi, Hassan ya bayyana cewa shi ne ya jagoranci gudanar da hari a yankin Ughelli-Ozoro na jihar mai arzikin man fetur.

Ya kuma jagoranci jami’an ’yan sanda zuwa maɓoyarsa a wani daji da ke Ozoro. A can jami’an sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da tarin alburusai huɗu da harsashi guda talatin da biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
  • Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
  • Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
  • Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas
  • Zan Ci Gaba Da Ɓata Wa Masu Sukar Tinubu Rai Da Ayyuka – Wike
  • IPOB A Najeriya Ta Jawo Asarar Rayuka Kimani 700 Da Kuma Kudade Kimani Naira Triliyon N7.5 Tun Shekara ta 2021