Aminiya:
2025-05-21@21:58:47 GMT

An kama mutane 13 kan zubar da ciki a Bauchi

Published: 25th, April 2025 GMT

Wasu mutane 13 sun faɗa a komar ’yan sanda ka zargi da zubar da ciki da kuma mutuwar wata budurwa ’yar shekara 18 a Jihar Bauchi.

Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Mohammed Ahmed Wakil, ya ce ana tuhumar huɗu daga cikin mutanen da aikata laifin fyade, zubar da ciki da kuma mutuwar budurwa a garin Misau da ke Ƙaramar Hukumar Misau.

Wakil ya ce, a ranar 4 ga Afrilu, 2025 sun samu bayanai ewa, kimanin watanni hudu da suka gabata, wasu matasa biyu a yankin Lariski da ke Misau, sun kama wata yarinya mai shekaru 18 da suka yi ta yi lalata da ita sau da yawa.

Ya ce a lokacin da suka lura tana ɗauke da juna biyu, sai suka nemi wani mutum suka ba shi naira 40,000 don ya taimaka musu wajen zubar da cikin, amma abin takaici sai aka samu matsala wanda a qarshe ya yi sanadiyyar mutuwarta.

Wakil ya ce, “Bayan an yi mata allurar zubar da ciki saita fita daga hayyacinta, daga baya kuma ta kamu da rashin lafiya. Hakan ya sa danginta suka kai ta Babban Asibitin Misau, daga baya an mika ta zuwa Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya (FMC) da ke Azare, inda hukumomin asibitin suka sanar da cewa ta mutu a lokacin da take jinya.”

Bayan samun rahoton, an kama wadanda ake zargin, inda suka amsa laifin da suka aikata tare da ambaton wasu da ke da hannu a lamarin.  Ya ce sauran wadanda ake zargin da wasu mutum huɗu suna hannun ’yan sanda ana bincike.

Bayan haka kuma za a gurfanar da su a gaban kuliya bisa laifukan da suka aikata.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Zubar da ciki zubar da ciki

এছাড়াও পড়ুন:

Wulayati Ya Ce Samun Kalamai Masu Karo Da Juna Tsakanin Trump Da Mukarrabansa Yana Zubar Da Kwarin Gwiwa

Mai ba da shawara ga jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Kalamai masu karo da juna na Trump da mataimakansa sun zubar da kwarin gwiwa ga gwamnatin Amurka

Mai bai wa Jagoran juyin juya halin Musulunci shawara ya bayyana cewa: Sabani da ake ci gaba da yi a cikin maganganu da ayyukan Trump da takwarorinsa na haifar da rashin amincewa da gaskiyar gwamnatin Amurka.

Ali Akbar Velayati mashawarcin Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran ya yi tsokaci a cikin wani sako da ya wallafa a dandalin X kan kalamai masu cin karo da juna da jami’an Amurka suka yi.

Mai bai wa Jagoran juyin juya halin Musulunci shawara ya ce ci gaba da cin karo da juna a cikin maganganu da ayyukan Trump da mukarrabansa ya haifar da rashin amincewa da gaskata gwamnatin Amurka.

Velayati ya kara da cewa: Wannan batu ba a taba ganin irinsa ba a tarihin diflomasiyya a duniya kuma yana nuni da halin da ake ciki a cikin gwamnatin Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatan wutar lantarki sun tsunduma yajin aiki a Kano
  • Wulayati Ya Ce Samun Kalamai Masu Karo Da Juna Tsakanin Trump Da Mukarrabansa Yana Zubar Da Kwarin Gwiwa
  • Queen Zeeshaq za ta shiga daga ciki
  • Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo
  • ‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja
  • Yadda aka kashe dan fashi aka kama wasu 7 a Abuja
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wani Kasurgumin Barowon Shanu Da Garkuwa Da Mutane A Kasuwar Shinge
  • Sharhin Bayan Labarai: Dandalin Tattaunawa Na Tehran
  • Everton Ta Yi Ban Kwana Da Goodison Park
  • Mutane 7 Sun Mutu 11Sun Jikkata A Hadarin Mota A Niger.