Leadership News Hausa:
2025-11-18@09:04:16 GMT

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

Published: 3rd, October 2025 GMT

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

Wani abu da ya ja hanklan mutane shi ne, irin muggan makaman da ‘yan bindigar suka hallara da su a wajen kulla yarjejeniyar, wadanda kuma babu wani mahaluki da ke da ikon kwace makaman daga hannunsu, a yayin kulla yarjejeniyar, ta jeka nayi ka.

Kazalika, a cikin daya daga cikin faifan Bidiyon, an ga yadda daya daga cikin shuwagabannin ‘yan bindigar ya yi bazaranar shedawa gwamnati da sauran jami’an gwamnatin da suka halarci wajen kulla sulhun cewa, idan har gwamnati ta kuskura ta kashe ‘yan bindiga dubu goma, suma za su hallaka adadin mutane kamar hakan.

Wasu ‘yan Nijeriya dai, sun yi ittifakin cewa, kasar nan, ta koma tamkar, a hanun tafin ‘yan bindigar.

Kulla wannan yarjeniyra dai, ta nuna a zahiri na irin gazawar da shuwagannin wadannan kananan kananan hukumomin na jihar ta Katsina.

Mun sha bayyana cewa, yin yarjejeniya da ‘yan bindiga ba a ba ce, da za ta kasance ta dogon zango ba.

Hujjar da zamu iya kafawa a nan ita ce, a lokacin mulkin tsohon gwamnan Jihar Katsina Aminu Bello Masari, tsohuwar gwamnatinsa ta yi sulhu da su, wanda har mazauninsu ya same su ya dauki hotuna tare da su da kuma raba masu da kudade, amma daga baya, abin da ya biyo baya shi ne, suka ci gaba da hallaka rayukan jama’ar jihar.

Bugu da kari, a Jihar Zamfara, a lokacin tsohowar gwamnatin gwamna Mohammed Matawalle wanda a yanzu shi ne, karamin ministan tsaro, ya bai wa ‘yan bindigar damar yi masu afuwa, duk da cewa, wadannan miyagun, sun hallaka rayukan jama’a da yi wa mata fyade da tarwatsa wasu al’ummomi daga garuruwansu da kuma sace dubban mutane.

Tsohuwar gwamnatin Matawalle, ta dauki wancan matakin ne, bisa yakinin cewa, ‘yan bindigar za su ajiye makamansu su kuma rungumi yin sulhu da gwamnatin, amma har yanzu, ba su dakatar da aikata ta’asar ta su ba, musamman duba da cewa, har yanzu jihar na ci gaba da fuskantar hare-harensu.

Hakazalika, gwamnan Jihar Katsina Dikko Umar Radda wanda ya gaji tsohon gwamann jihar Masari da kuma takwaransa na Jihar Zamfara, Lawal Dauda Dare, wanda ya gaji tsohon gwamnan jihar Matawalle, suka kesa kasa da cewa, atabau, ba za su kulla wata yarjejeniyar sulhu da ‘yan bindigar ba.

Sai dai, da alamu Radda ya sauya na sa ra’ayi, wanda hakan ya bai wa kananan hukumomin jiharsa su sha daya kulla yarjejeniyar da ‘yan bindigar domin samar da zaman lafiya, a tsakanin alumominsu.

A nan dai, koma dai menene ra’ayin mu a nan, wannan yarjejeniyar da ‘yan bindigar da suka dauki ran muane tamkar ba komai ba da karbar kudin fansa daga gun ‘yanuwan wadanda suka sace ‘yanuwansu da tarwatsa al’umomi daga muhallansu wannan ya nuna irin asalin gazawa daga bangaren gwamnatin jihar ta Katsina.

Har yanzu dai, akwai dimbin tambayoyi dangane da wannan yarjejeniyar ta jeka na yi ka, domin hakan ya nuna a zahiri na gazawar gwamnatin jihar na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan jihar.

Matsayin a wannan Jaridar shi ne, yarjejeniyar da ‘yan bindigar aba ce da har yanzu ba ta sauya zani ba, kuma zai yi wuya hakan ta faru, domin a nan, muma bama goyon bayan hakan.

Shi ma wai, ta wacce fuska ce, za a kwantarwa ‘yanuwan wadanda ‘yan bindiga suka halka masoyansu da cin mutuncinsu da yi masu fyade da kuma aikata masu nau’ukan ta’asa da ban da ban.

Kazalika, wannan kulla yarjeniyar ta nuna irin gazawar da jami’an tsaro suka da ita ko da yake dai, wasu na yin tsegumin cewa, shiga aikin na tsaro tamkar ya koma ne wata hanya ta neman kudi a kasar.

A nan muna nuna damuwar da cewa, wannan kulla yarjejeniyar tamkar zuba kima da mutuncin Nijeriya ne, a idon duniya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kulla yarjejeniyar yan bindigar

এছাড়াও পড়ুন:

Mahara sun kashe matan aure sun ƙona gidansu a Kano

Wasu mahara sun yi wa wasu matan aure biyu kisan gilla a gidan mijinsu da keunguwar Tudun Yola a Ƙaramar Hukumar Gwale ta Jihar Kano.

Aminiya ta samu rahoton cewa maharan banka wa gidan wuta bayan da suka soka wa ɗaya daga cikin matan wuka har lahira, ɗayar kuma an tsinci gawarsa a cikin banɗaki.

Matan da aka yi wa wannan kisan gilla — Hauwa’u Yakubu da Zahra’u Aliyu — mata ne ga wani mai suna Alhaji Ashirin Shu’aibu Usaini.

Al’unnar unguwar Tudun Yola sun shiga tashin hankali da wannanan ɗanyen aiki.

HOTUNA: Yadda Babban Taronjam’iyyar PDP ke gudana Mayaƙan ISWAP sun sace Janar sun kashe sojoji a Borno

Ɗan mai gidan, Anas Shu’aibu, ya yi zargin ana yi wa matan mahaifinsa wannan kisan gilla ne da tsakar rana lokacin da mai gidan da ’ya’yansa suka fita.

“Ba mu san abin da ke faruwa ba sai da daddare bayan mahaifinsmu ta kira cewa ina dawo gida, muna zuwa muka ga ɗaya yaqar a ƙone, ɗayar muka an kulle ta a banɗaki, ko da muka ɓalle ƙofar sai muka samu ita ma ta riga ta mutu.

“Da farko mun yi zargin gobara ce, amma sai muka lura cewa da alamar hari aka kai musu.”

Alhaji Shu’aibu, cikin kaɗuwa ya bayyana cewa “sun kashe Matana, sun ƙona gawar ɗayar. Ban san dalilin wannan rashin imani ba.”

Kakakin ’yan sandan Jihar Kano, CSP Abdullahi Haruna Koyawa ya tabbatar da faruwar lamarin tare da cewa rundunar ta ta fara gudanar da bincike a kai.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • GGCSS Maga: Halin da iyaye ke ciki bayan sace ’ya’yansu
  • ’Yan Majalisar Dokokin Taraba 16 sun sauya sheka daga PDP zuwa APC
  • ’Yan bindiga 5 Sun shiga hannun ’yan sanda a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara
  • DRC: An Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Tsakanin Gwamnati Da Kungiyar M23
  • Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
  • Fintiri ya yi watsi da korar Wike daga PDP
  • Mahara sun kashe matan aure sun ƙona gidansu a Kano
  • Yadda ’yan bindiga suka kashe banga 16 suka sace mutane 42 a Neja
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yanga 16 sun sace mutane 42 a Neja