Mata Ne Ƙashin Bayan Gyaran Duk Wata Al’umma, In Ji Sheik Shamsudeen
Published: 21st, September 2025 GMT
Haka nan a nasa ta’alikin da ya gabatar Malam Abubakar Abba Dewu ya jawo hankalin Malaman Islamiyoyi, domin su kasanca masu shirya irin wadanan muhadirorin lokacin Bayan lokacin a Makarantun su, domin cusawa Mata da ƙananan yara jin Tsoron Allah tare da yin abin da ya dace da koyarwar addinini Musulunci a bisa sunnar Annabi Muhammad (saww).
Haka nan a lokacin da take miƙa jawabi godiya a gun taron Shugaban Makaranta Malam Halima Musa ta ce, suna shirya irin wannan muhadaran ne lokaci bayan lokacin sabo da cusawa Mata da ƙananan yara tsoron Allah a zukata.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An ƙone al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
Ana zargin wata matar aure, Rabi Nuhu da ke garin Magama Gumau a ƙaramar hukumar Toro ta Jihar Bauchi, da cin zarafin wata yarinya ’yar shekara biyar ta hanyar ƙone mata al’aura, saboda zargin tana yawan yin fitsarin kwance.
Wakilinmu ya gano cewa yarinyar marainiya ce wadda mahaifiyarta ta rasu kusan shekara ɗaya da ta gabata, inda take zaune tare da mahaifinta, Mohammed Umar, da matarsa.
CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100 Mahara sun kashe ɗan sanda sun ɗauke bindigarsa a TarabaWani mai fafutukar kare haƙƙin bil’adama a garin, Kabiru Abdulkadir, ya bayyana cewa sai bayan kwana biyar da ƙonewar ta faru ne al’amarin ya bayyana.
“Don guje wa matsala, mahaifin yarinyar ya sayi wata katifa ta daban domin ta riƙa kwanciya a kai, amma duk da haka matar tasa ba ta daina azabtar da yarinyar ba,” in ji Kabiru.
Aminiya ta ruwaito cewa, lamarin ya bayyana ne lokacin da yarinyar ta roƙi kawunta ya saya mata katifa, inda ta shaida masa cewa mamanta ta ƙona al’aurarta saboda yawan fitsarin kwance, dalili ke nan da ya yi wa ’yan sanda ƙorafi.
Kazalika, ana zargin cewa duk lokacin da matar ta samu sabani da mijinta, sai ta huce fushi a kan yarinyar.
Da yake jawabi, mahaifin yarinyar, Mohammed Umar, wanda ke aiki da wani gidan talabijin, ya tabbatar da cewa matarsa ta kan yi ƙorafi kan yawan fitsarin kwancen yarinyar, abin da ya sa ya saya mata katifa ta daban.
Umar ya ce: “A farko, da na ga ƙuna a jikinta, matata ta shaida min wai shayi mai zafi ne ya zubo a jikinta. A lokacin na gaskata hakan, har sai da na lura da ciwon yana ƙaruwa.”
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, CSP Mohammed Wakil, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa rahoto ya iso ofishin su da misalin ƙarfe 3:00 na ranar 13 ga Satumba, 2025.
Wakil ya ce yarinyar ta sami ƙonuwa a ƙasan cikinta, cinyoyinta, da kuma al’aurarta.
Ya ƙara da cewa, kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Sani Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin a gaggauta kama matar tare da miƙa ta zuwa sashen manyan laifuka domin gudanar da cikakken bincike.
Ya bayyana cewa da zarar an kammala binciken, za a gurfanar da ita a gaban kotu.