Aminiya:
2025-09-20@20:20:49 GMT

Bayan biyan N50m an sako ma’aurata da ’yarsu su da aka sace a Katsina

Published: 20th, September 2025 GMT

Sama da mako uku da suka gabata, wasu ’yan bindiga suka yi garkuwa da wani magidanci da matarsa mai juna biyu da kuma ’yarsu a unguwar Kanada da ke Ƙofar Ƙaura a garin Katsina.

Masu garkuwar sun fara neman a biya su naira miliyan 100 kafin su sako su, amma daga baya aka daidaita da su a kan naira miliyan 50.

Mahaifin Halimatu, Alhaji Ali Turare, ya tabbatar da biyan kuɗin kafin a sako ’yarsa da mijinta da jikarsa.

“Bayan kwana uku da biyan kuɗin ne suka kira mu ta waya, suka ce an sako su, a je a karɓe su a Gurbin Ɓaure. Yanzu haka duk suna asibiti ana duba lafiyarsu,” in ji shi.

Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto babu wani bayani da ya fito daga bakin rundunar ’yan sandan jihar Katsina game da lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Garkuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

 

Kamfanin dillancin labaran Nijeriya ya bayar da rahoton cewa, lamarin wanda ya faru ne a lokacin da ake gudanar da aikin a ƙarshen mako a masana’antar, ya yi sanadin mutuwar ma’aikata biyu ciki har da wani jami’in soji da ke aiki tare da jikkata wasu huɗu.

 

“Na ji wani babban ƙara har sai da ya girgiza gine-ginen da ke kewayen DICON. Mutane na ta gudu daga wurin, amma muna tunanin fashewar bam ne, amma daga baya mun gano cewa daga masana’anta ne,” inji wani mazaunin da ya nemi a sakaya sunansa.

 

Shaidun gani da ido sun ce fashewar na da nasaba da samar da hoda mai matukar muhimmanci wajen ƙera hodar harsashi ga sojojin Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna
  • Bayan biyan N50m ma’aurata da ’yarsu su da aka yi garkuwa da su a Katsina
  • Takari: Rayuwar baƙin haure ’yan Najeriya mazauna Saudiyya
  • Fubara ya sauka a filin jirgin saman Fatakwal
  • Wani ya sace munduwar Fir’auna a gidan tarihin Masar
  • Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja
  • ’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa
  • Gwamnatin Tarayya ta raba wa talakawa N330bn — Ministan Kuɗi
  • ’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m