Nau’o’in Jirage Uku Sun Kammala Sauka Da Tashin Farko Bisa Taimakon Majaujawar Maganadisu A Jirgin Dako Na Fujian Na Kasar Sin
Published: 23rd, September 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe ya kaddamar da aikin samar da wutar lantarki ta hasken rana mai ƙarfin megawat 1 a garin Talasse, karamar hukumar Balanga.
Aikin, wanda aka kulla ta hanyar haɗin gwiwa tsakanin Hukumar Samar da Wutar Lantarki a Karkara (REA), Bankin Duniya, da kamfanin MIDS Dynamics, na da aniyar samar da wutar lantarki ba tare da yankewa ba ga sama da gidaje 8,000 a Talasse da kauyuka makwabta, idan aka kammala shi cikin watanni huɗu.
Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a Indonesia Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800A wajen bikin kaddamar da aikin, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana shi a matsayin muhimmin ci gaba a shirin gwamnatinsa na bunƙasa makamashi mai tsabta, araha da kuma dorewa.
“Wannan aiki ba kawai zai ba da haske ga gidaje ba ne kawai, zai ƙarfafa kasuwanci, ya samar da ayyukan yi, kuma ya kawo ci gaban tattalin arziki a yankin,” in ji Gwamnan.
Ya ƙara da cewa aikin ya nuna nasarar haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu wajen ci gaban fannin makamashi, tare da yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa gyare-gyaren da yake kawo wa fannin wutar lantarki, musamman Dokar Wuta ta 2023, wadda ta bai wa jihohi damar tsara hanyoyin samar da makamashinsu.
Shugaban REA, Injiniya Abba Aliyu, ya jinjina wa Gwamna Inuwa bisa hangen nesa da jajircewarsa wajen inganta makamashi a jihar, inda ya ce hukumar na shirin aiwatar da ƙarin ayyukan sola a ƙananan hukumomi 10 na jihar.
A nasa bangaren, Shugaban MIDS Dynamics, Injiniya Halis Mohammed, ya bayyana Gombe a matsayin jiha ta farko a Najeriya da ta bayar da kuɗin haɗin gwiwa don irin wannan aiki, kuma jagora a sauyin makamashi.
Shugabannin yankin, ciki har da Bala Waja, Alhaji Mohammed Danjuma Mohammed, da Dan Majalisa Musa Buba, sun gode wa Gwamnan bisa cika alkawarin da ya ɗauka, tare da alƙawarin kare aikin daga lalacewa da satar kayan aiki.
“Mun daɗe muna jiran wannan rana. Yanzu haske ya dawo cikin ƙasar Waja,” in ji ɗaya daga cikin shugabannin yankin.