Kwalara ta kashe mutane 58, wasu sun kamu a Bauchi
Published: 20th, September 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Bauchi ta sanar mutuwar mutane 58 sanadiyyar kamuwa da cutar amai da gudawa (kwalara) inda ta gano sabbin masu dauke da cutar mutane 258, wanda aka samu a kananan hukumomi 14 cikin 20 na jihar.
Duk shugaban da bai yi aiki ba bai kamata a sake zaɓarsa ba — Jonathan An tsinci gawar kwamandan hukumar NDLEA a otel a KalabaMataimakin gwamnan jihar, Alhaji Muhammadu Auwal Jatau ne ya bayyana haka a lokacin da yake kaddamar da kwamitin kula da cutar kwalara na jiha, da kuma kwamitin kwararru kan yaki da cutar.
Jatau ya bukaci mambobin kwamitocin da su tunkari ayyukan da aka dora musu cikin kishi da kwarewa da kuma hanzari.
Mataimakin Gwamnan wanda shi ne shugaban kwamitin ya koka kan yadda cutar kwalara da ta sake barkewa, kuma tana ci gaba da janyo asarar rayuka, da kuma kawo cikas ga harkokin rayuwa da kuma kawo kalubalen ga tsarin kiwon lafiyar jihar.
Ya ce, cutar kwalara na daya daga cikin manyan cututtuka da ke barazana ga lafiyar al’umma, duk da kokarin da gwamnatin jihar da takwarorinta ke yi na shawo kan cutar.
Jatau ya bayyana cewa, kafa kwamitoci yana da mahimmanci wajen cimma manufofin da ake so.
“Ana iya yin rigakafin wadannan bullar cutar tare da daukar matakan da suka dace,, da kuma ci gaba da inganta tsaftar ruwan sha tsaftar muhalli, da tsaftar jiki.”
A kan haka ne ake sa ran kwamitin zai yi aiki tare da kungiyoyin hadin gwiwa don shawo kan matsalar.
Ya ce, Jihar Bauchi ta mayar da hankali kan barkewar cutar kwalara da kuma fitar da dabarun rigakafin cutar kwalara na dogon lokaci tare da tsare-tsare da tsare-tsare na kasa da kasa kan tsare-tsaren dakile cutar kwalara a Najeriya da yin rigakafi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnati Kwalara cutar kwalara
এছাড়াও পড়ুন:
Jigawa Na Gabatar Taro A Abuja Domin Tattara Bayanin Kasafin Kudin 2026
Ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsare ta jihar Jigawa, ta shirya taron yini daya a birnin tarayya tare da hadin gwiwar ELIP kungiyar farar hula ta musamman, domin tattara kayan aiki na kasafin kudin 2026.
A nasa jawabin kwamishinan kasafin kudi da tsare-tsare na jihar Alhaji Ibrahim Babangida Umar Gantsa ya bayyana mahimmancin taron, inda ya ce abubuwan da masu ruwa da tsaki suka yi na da matukar muhimmanci.
Babangida Gantsa wanda ya samu wakilcin Daraktan SDG na ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsare ta jiha, Alhaji Basiru Nasoro ya bukaci masu ruwa da tsaki su samar da bayanai masu ma’ana.
A nasa jawabin, Alhaji Najibullah Ahmad wanda masanin kasafin kudi ne ya bayyana cewa, makasudin shi ne a jawo hankalin ‘yan kasa da jawo hankalinsu tare da samar da gaskiya da rikon amana a cikin tsarin kasafin kudi.
A cewarsa, taron zai kuma baiwa masu ruwa da tsaki damar zakulo wuraren da suka fi ba da fifiko da kuma taimakawa gwamnati wajen yanke shawara, tare da samar da yanayi mai kyau na sanin ya kamata.
Najibullah ya yi nuni da cewa, taron zai kuma bayar da rahoto na shekara-shekara kan yadda kudaden jama’a suka kasance kuma za a ware domin biyan bukatun jama’a.
Shima da yake jawabi, Alhaji Isa Mustapha wanda shi ma ma’aikaci ne a ma’aikatar, ya bayyana cewa tsarin kashe kudi na matsakaicin zango, ya samar da cikakken tsari.
A cewarsa, tsarin ya yi daidai da shirye-shiryen gwamnati, tallafin masu ba da tallafi da kuma shirye-shiryen kamfanoni masu zaman kansu don cimma manufa guda.
Alhaji Ayuba Doro Gwaram, wakilin ELIP wanda ya gabatar da jawabi kan abubuwan da ‘yan kasa suka zaba a shekarar 2024, inda ya yi nazarin abubuwan da ‘yan kasa ke nunawa a cikin kasafin kudin 2025.
Ayuba ya ce, an gabatar da bayanai 1,105, sannan 548 sun bayyana a cikin kasafin, wanda ya nuna kashi 49 cikin 100 na jimillar abubuwan da aka gabatar.
Ya yi nuni da cewa, abubuwan da aka samu sun nuna kashi 26.8 cikin 100 na jimillar kasafin kudi na Naira biliyan 175.442 na jihar Jigawa a shekarar 2025, wanda hakan ya nuna cewa abin da ‘yan kasa ke amfani da shi ya haura na shekarar 2023 a fannin kudi.
Ayuba ya yi nuni da wasu daga cikin kalubalen da suka hada da rashin sa ido kan ayyukan, rashin karkatar da albarkatun kasa da kuma wahalar daidaita bukatu da bukatu a fagen dimokuradiyya.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, wasu kungiyoyin CSO da na kananan hukumomi sun bayar da bayanai daban-daban a taron majalisar dattijai da ya kunshi kananan hukumomi 7 na jihar Jigawa.
KARSHE/USMAN MZ