Aminiya:
2025-09-20@18:56:07 GMT

Wata mata ta haifi ’ya’ya huɗu a Bauchi

Published: 20th, September 2025 GMT

Wata mata ta haifi jarirai huɗu — maza biyu da mata biyu — a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Tarayya ta Kimiyyar Kiwon Lafiya (FUHSTHA) da ke Azare, a ranar Alhamis, 18 ga Satumba, 2025.

Sakataren yaɗa labarai na asibitin, Abdu Mohammed, ya shaida wa Aminiya cewa Malama Hauwa ta haifi yaran ne ta hanyar tiyata, kuma tana ci gaba da jinya tare da ’yan huɗun.

A washegarin haihuwar, Hajiya Halima Garba, matar shugaban asibitin (CMD), ta ziyarci mai jegon tare da mijinta da manyan ma’aikatan asibitin.

Ta taya iyalan murna tare da addu’ar samun lafiya cikin gaggawa.

’Yan bindiga sun kashe basarake, sun tarwatsa mutane a Sakkwato Kwalara ta kashe mutane 58, wasu sun kamu a Bauchi

Kamar yadda ta saba a duk lokacin da aka samu irin wannan lamari, Hajiya Halima ta bayar da tallafin kuɗi, kayayyakin jinya da kayan jarirai domin taimaka wa iyalin. Ta kuma bai wa wasu majinyata tallafin kuɗi.

Shi Dakta Dauda Abubakar Katagum, ya taya iyalan murna, inda ya bayyana haifuwar jariran huɗu a matsayin baiwa da kyauta daga Allah.

Angon ƙarni, Buba Adamu, wani manomi daga ƙauyen Gambaki a ƙaramar hukumar Katagum, ya bayyana farin cikinsa tare da godiya bisa karamcin da aka yi musu.

A matsayin nuna godiya, ya sanya wa ɗaya daga cikin jariran mata suna Halimatu Sa’adiyya, wato takwara ga uwargidan CMD.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan huɗu

এছাড়াও পড়ুন:

An cafke mutum 6 kan tono gawa a kabari don yin asiri a Gombe

Hukumar Sibil Difens (NSCDC) a Jihar Gombe, ta kama mutum shida bisa zargin tono gawar wani mutum a kabari tare da cire sassan jikinta domin yin asiri.

Ɗaya daga cikin waɗanda aka kama, Kawuji Sarki, mai shekaru 39, ya amsa laifin.

Wata mata ta ƙona al’aurar ’yarta da wuta kan zargin maita a Bauchi Janye Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya koma Ribas

Ya bayyana cewa wani mutum mai suna Aliyu Chindo ne, ya ba su aikin cire idanun mamacin, tare da yi wa kowannensu alƙawarin Naira 500,000.

Sai dai ya ce bayan kai masa sassan jikin, Chindo ya gudu ba tare da ya biya su ba.

Nan take jami’an tsaro suka cafke su.

An gano cewa sun tono kabarin wani tsoho mai shekaru 85, Mallam Manu Wanzam, wanda aka binne a ranar 9 ga watan Satumba a maƙabartar Gadam Arewa da ke Ƙaramar Hukumar Kwami.

Kakakin NSCDC a jihar, SC Buhari Sa’ad, ya bayyana sunayen sauran da aka kama: Adamu Umar (22), Umar Jibrin Aboki (21), Abdullahi Umar Dauda (17), Muhammed Isa Chindo (28), da Manu Sale (23).

Ya ƙara da cewa ana ci gaba da neman Aliyu Chindo da ya tsere.

Kwamandan hukumar a jihar, Jibrin Idris, ya bayyana lamarin a matsayin “rashin imani,” tare da tabbatar da cewa za su gurfanar da waɗanda suka kama a kotu bayan kammala bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwalara ta kashe mutane 58, wasu sun kamu a Bauchi
  • Wata mata ta ƙone fuskar ’yar mijinta da tafasasshen man girki a Borno
  • An cafke mutum 6 kan tono gawa a kabari don yin asiri a Gombe
  • Wata mata ta ƙona al’aurar ’yarta da wuta kan zargin maita a Bauchi
  • Wata mata ta ƙona farjin ’yarta da wuta kan zargin maita a Bauchi
  • Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
  • Cutar Kwalara ta kashe mutum 58 a Bauchi
  • Kasar Albania ta nada mutum-mutumi a matsayin minista
  • Gwamnatin Tarayya ta raba wa talakawa N330bn — Ministan Kuɗi