Wata mata ta haifi ’ya’ya huɗu a Bauchi
Published: 20th, September 2025 GMT
Wata mata ta haifi jarirai huɗu — maza biyu da mata biyu — a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Tarayya ta Kimiyyar Kiwon Lafiya (FUHSTHA) da ke Azare, a ranar Alhamis, 18 ga Satumba, 2025.
Sakataren yaɗa labarai na asibitin, Abdu Mohammed, ya shaida wa Aminiya cewa Malama Hauwa ta haifi yaran ne ta hanyar tiyata, kuma tana ci gaba da jinya tare da ’yan huɗun.
A washegarin haihuwar, Hajiya Halima Garba, matar shugaban asibitin (CMD), ta ziyarci mai jegon tare da mijinta da manyan ma’aikatan asibitin.
Ta taya iyalan murna tare da addu’ar samun lafiya cikin gaggawa.
’Yan bindiga sun kashe basarake, sun tarwatsa mutane a Sakkwato Kwalara ta kashe mutane 58, wasu sun kamu a BauchiKamar yadda ta saba a duk lokacin da aka samu irin wannan lamari, Hajiya Halima ta bayar da tallafin kuɗi, kayayyakin jinya da kayan jarirai domin taimaka wa iyalin. Ta kuma bai wa wasu majinyata tallafin kuɗi.
Shi Dakta Dauda Abubakar Katagum, ya taya iyalan murna, inda ya bayyana haifuwar jariran huɗu a matsayin baiwa da kyauta daga Allah.
Angon ƙarni, Buba Adamu, wani manomi daga ƙauyen Gambaki a ƙaramar hukumar Katagum, ya bayyana farin cikinsa tare da godiya bisa karamcin da aka yi musu.
A matsayin nuna godiya, ya sanya wa ɗaya daga cikin jariran mata suna Halimatu Sa’adiyya, wato takwara ga uwargidan CMD.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan huɗu
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta yi Watsi Da Zargin Da Amurka Tayi Mata Kan Batun Motocin Agaji A Gaza
Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar gwagwarmaya ta Hamas tayi watsi da zargin da Amurka ta yi mata a baya bayan nan na cewa mayakanta sun wawushe kayayyakin agaji da wata mota take dauke da shi a yankin Gaza, ta bayyana zargin a matsayin karyace kawai mara tushe balle madafa, tace Amurka na wannan zargin ne domin fakewa da shi wajen takaita shigar da kayyakin agaji a yankin gaza,
Wannan yana nuna karuwar takaddama tsakanin Amurka da sauran bangarorin falasdinawa kan batun samar da kayayyakin agaji da kuma daukar nauyin da ya rataya a wuyansu, gannin yadda tallafi yayi karance kuma kayayyakin more rayuwa sun tabarbare don haka irin wadannan zarge-zarge na iya kara tsananin rashin yarda da kuma kawo cikas a kokarin da ake yi na kai kayayyakin agaji zuwa yankin.
Mashahanta suna kallon labarin Amurka a matsayin wani bangare na parfagandar na canza sunan Hamas da kuma share fagen kwance dammararta, suna ganin cewa wannan ikirarin yana zuwa ne a daidai lokacin da ake kokarin diplomasiya don canza yanayin tsarin gwamnati bayan yakin Gaza, da kuma raunana kungiyoyin gwagwarmaya karkashin kula da aikewa da kayayyakin agaji da aka bujiro da shi
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai November 3, 2025 Iran Ta Karbi Sako Kan Batun Komawa Teburin Tattaunawa Ba Kai Tsaye Ba November 3, 2025 Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher November 3, 2025 Pezeshkian: Bunkasa Masana’antar Makamashin Nukiliyar Iran Don Inganta Rayuwar Al’ummar Iran Ne November 2, 2025 Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran November 2, 2025 Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani November 2, 2025 Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza November 2, 2025 Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci