Leadership News Hausa:
2025-09-20@14:29:09 GMT

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

Published: 20th, September 2025 GMT

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

Wasu mazauna ƙauyen Zalla Bango a ƙaramar hukumar Sabon Birni, Jihar Sokoto, sun rasa rayukansu a wani haɗarin jirgin ruwa yayin da suke tserewa daga harin ƴan bindiga. Lamarin ya faru ne da yammacin Alhamis, 18 ga Satumba, lokacin da Kwale-Kwalen da ke ɗauke da jama’a yayi karo da dirkar gadar ruwa da ta rushe a kan hanyar Goronyo–Sabon Birni, hakan ya haddasa fashewarsa sannan ya nutse.

Shaidu sun bayyana cewa mafi yawan waɗanda abin ya rutsa da su mata ne da suka hau jirgin cikin gaggawa don tsallaka ruwa, su kuɓuta daga harin da ake tsammani an kai musu. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da jama’a ke ci gaba da barin gidajensu saboda hare-haren ƴan bindiga masu yawa a yankin.

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Shugaban ƙaramar hukumar Sabon Birni, Alhaji Ayuba Hashimu, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce adadin waɗanda suka mutu har yanzu ana bincike, sai dai an samu gawar mace guda ɗaya. Ya bayyana cewa jami’ai suna ci gaba da aikin ceto da neman sauran waɗanda suka bace.

Lamarin ya ƙara nuna irin mummunan tasirin rashin tsaro a Sokoto ta Gabas. A kwanakin baya ma, mutane shida sun mutu a Garin Faji bayan jirgin ruwa ya kife yayin da suke gudun harin ƴan ta’adda, yayin da ƴan bindiga kuma suka kashe wasu shida a Kwanar Kimba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Ɗantsoho Ya Mayar Da Hankali Wajen Farafaɗo Da Martaba Da Ƙimar NPA

Daga baya an ƙara nata wani nauyin kula da Tashoshin Warri, Koko, Burutu da kuma ta Sapele, waɗanda kamfanonin ƴ an kasuwa masu zaman kansu ne, ke tafiyar da su, amma har zuwa yau, mahukunta a NPA ne, ke tafiyar da duk wata ragamar hukumar baki ɗaya.

A shekaru da dama da suka gabata, matsaloli da dama, sun dabaibaye NPA da suka haɗa da, cin hanci da rashawa da rashin ingantattun kayan aiki, musamman na zamani da sauransu, inda waɗannan matsalolin suka haifar wa da NPA koma baya matuƙa, musamman na wajen zama a kan gaba wajen gudanar da harkar hada-hadar kasuwanci a nahiyar Afirka.

Amma, za mu iya cewa, Allah san barka da naɗa Dakota Abubakar Ɗantsoho, a matsayin zaƙaurin shugaban hukumar kuma mai hangen nesa, wanda ya a baje ƙwarewarsa da kuma hazaƙarsa da su yi daidai da ƙugurin shugaba Bola Ahmed Tinubu na sake farfaɗo da fatan ga ƴ an ƙasar da kuma ita ƙasar Kant’s, wato Renewed Hope Agenda.

Ɗantsoho, da shigarsa ofis, bai wani ɓata lokaci ba, ya fara da ƙaddamar da gagarumin bincke domin gano inda ake da giɓi kan gudanar da ayyukan a NPA wanda hakan ya ba shi damar, yin garanbawul baki ɗaya a hukumar, musamman domin ya sake ɗora ta, a kan turba, mai ɗorewa.

Domin tabbatar da ya daƙile ƙalubalen cunkoson musamman na Jiragen Ruwa da ke sauka, Ɗantsoho ya yi ƙoƙari wajen ganin, an yi nesa da hanyoyin  Tashar Jiragen Ruwa ta jihar Legas da Tashoshin Jiragen Ruwa na Fatakwal da ta Onne da ta Warri da kuma ta Kalaba musamman duba da cewa, rashin ɗaukar wannnan matakin tun da farko a baya, ya haifar da cunkoso da ya kai kaso 90

Kazalika, baya ga magance wannan matsalar ta cunkoso da shugaban ya yi,hakan ya kuma sanya hada-hadar kasuwanci a yankunan da ke a nahiyar Afirka, ƙara tunbatsa.

Ɗantsoho, bai tsaya a nan ba,misali  saboda tsaikon da ake samu a Kogin Riba Neja, ya ƙirƙiro da aikin yashe hanyoyin ruwan, musamman domin a rage cunkoso da ake samu a Tashar Jiragen Ruwa ta Onitsha, wanda hakan ya taimaka wajen ci gaba amfana da albarkatun tattalin arziki.

Bugu da ƙari, saboda burin da ya ke da shi, musamman na zamantar ƙufurin ƙara ciyar da hukumar gaba, Ɗantsho ya tabbatar da an ware dala biliyan ɗaya domin a yiwa ginin Tashar Jiragen Ruwa ta Tincan Island da  ta Apapa da ta, Riɓers da ta Onne ta ta Warri da kuma ta garin Kalaba.

Asusun Bunƙasa Ayyuka wato RHIDF ne, ke tallawa wajen gudanar da waɗannan ayyukan wanda hakan ɗai ƙara taimaka wa wajen ƙara bunƙasa ɗuba hannun jari a fannin.

Hakazalika, a ƙarƙashin iya salon shugabanci na gari na Dakta Ɗantsoho ke ci gaba da gudanarwa, an samu raguwa cunkson Jiragen Ruwa da sauka a Tashshin da suka kai kaso  45.1 da kuma samun ƙaruwar shigo da Kwantainoni, da suka kai kaso 9.7 wanda hakan, ya ƙara haɓaka hada-hadar kasuwanci natuƙa.

Ɗantso ya kuma ƙirƙiro da tsarin yin amfani da na’urar  Electronic truck call-up wanda hakan, ya ƙara zamantar da ayyuka a Tashohin Jiragen Ruwan tare da kuma rage cunkoso, Jiragen Ruwa.

Ɗaukacin waɗannan ayyukan da Ɗantsoho ke gudanawar, sun zo ne, daidai da manufar gwamnatin shuigaba Bola Tinubu.

Shugaban na NPA ya kuma kasance a kan gaba wajen ganin an ƙaddamar da Tashin Tsayawar Jiragen Ruwa  na kan tudu, kamar dai, na gain Funtuwa, da ke a jihar Katsina, wnada an yi hakan ne, domin ƙara haɓaka fitar da kana da ba su shafi fannin Mai ba da kuma ƙara haɓaka hada-hadar kasuwanci.

Shirin aikin kashe dala biliyan ɗaya a Tashar Snake Island wanda za a ƙara faɗaɗa kadada 85 a cikin Tashar, an yi ne, bisa nufin gudanar da harkar hada-hadar kasuwanci a Tashar, wanda hakan zai kuma ƙara ɗaga darajar Nijeriya a fagne kasuwanci.

Ayyukan ci gaba da Ɗantsho ke ci gaba da samarwa a NPA, ba wai kawai nan ya tsaya ba, domin kuwa, a kwanan baya, an zaɓe shi ya zama shugaban ƙungiyar  kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Gabas da yankin Afirka ta Tsakiya wato PMAWCA.

Wannan zaɓar ta sa, ta nuna a zahiri, irin tunbatsar da ficen da ƙasar nan ta yi a fagen na harkar sufurin Jiragen Ruwa, musamman a nahiyar Afirka

Har ila yau, Ɗantsho shugaba ne, da bai yin wasa da kula da walwalar da haƙƙoƙin ma’aiakatasa, musamman domin ya tabbatar da yaƙi cin hanci da rasahawa.

Duk dai a ci gaba da marawa tsarin shugaba Tinubu na ci gaba da ƙara tarawa ƙasar kuɗaɗen shiga, Ɗantsoho ya amince da kafa tsarin tara kuɗaɗe shiga na kai tsaye, a NPA ta hanyar yin haɗaka da hukumar kula da harkokin sufurin jiragen ruwa ta ta ƙasa wato NIMAS da kuma hukumar Kwastam.

Wannan manufar, an yi ta ne, domin a tabbatar da ana bin diddigin tara kuɗaɗen shigar da kuma kula da su.

Ɗantsoho, ya kuma tabbatar da ana ƙara ƙarafafawa masu hada-hdar Jiragen Ruwa na ƙasar guiwa wanda kuma ya yi daidai da manufar gwamnatin ƙasar.

Burin da har zuwa yau Ɗantsoho ya sanya a gaba shi ne, ganin NPA ta tsarewa tsara, wajen ƙara samar da ci gaba ba wai kawai a tsakanin nahiyar Afirka ba, har a ma faɗin duniya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe basarake, sun tarwatsa mutane a Sakkwato
  • Yadda Ɗantsoho Ya Mayar Da Hankali Wajen Farafaɗo Da Martaba Da Ƙimar NPA
  • Fubara ya sauka a filin jirgin saman Fatakwal
  • Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja
  • SEMA Jigawa Da NEMA Da UNICEF Sun Bada Horo Akan Agajin Gaggawa A Auyo
  • Harin Makami Mai Linzami Yemen Ya Tilastawa Jirgin Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Saukar Gaggawa
  • An kashe ’yan ta’addan IPOB da yawa a Imo — ’Yan Sanda
  • ’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato