Leadership News Hausa:
2025-11-08@15:09:33 GMT

Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

Published: 21st, September 2025 GMT

Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

“Sanarwar jan hankaki – Taron bogi ‘convocation’ a Nijeriya – Jami’ar ba ta ba Dauda Kahutu Rarara digirin girmamawa ba”.

 

A yau (Lahadi) ne aka sanar da Jami’ar EAU labarin wani biki da kafafen yada labarai na Nijeriya suka rahoto ƙaryar cewa, Jami’ar ta gudanar da wani taro a ranar Asabar a Hotel din ‘NICON Luxury’ Abuja, Nijeriya.

 

Jami’ar ba ta ba da izinin gudanar da wani taro a wannan wuri a ranar ba, kuma an shirya wannan taron ne ta hanyar damfara ba tare da sanin ko izinin Jami’ar ba. Waɗanda suka shirya wannan taron sun yaudari wasu da yardar cewa suna wakiltar Jami’ar EAU, amma wannan gaba ɗaya ƙarya ce kuma ba su da ikon yin hakan, ko kuma karɓar kuɗi a madadin Jami’ar.

 

Jami’ar EAU ba ta ba Dauda Kahutu Rarara, Alhaji Ahmed Saleh jnr, Mustapha Abdullahi Bujawa da Tarela Boroh digirin girmamawa ba. Duk masu riƙe da digiri daga Jami’ar, za a iya samun sunansu kamar yadda aka jera a cikin Rajista na Digiri a https://europeanamerican.university/about/register-of-graduates

 

An ambaci sunan Musari Audu Isyaku a matsayin “Wakilin Arewacin Nijeriya na jami’ar”. Wannan mutumin ba shi da ikon wakiltar Jami’ar EAU kuma wannan taron da ya shirya, da bayar da digirin girmamawar duka ƙarya ce.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Jami ar EAU

এছাড়াও পড়ুন:

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

Ya ƙara da cewax gwamnatinsa ta fara gyara daga tushe, inda ilimi ya zama ginshiƙin farko. “Shekaru takwas kafin mu hau mulki, ɗalibanmu ba su samun takardun WAEC, sannan tsawon shekaru biyu suna fama da matsalar NECO. Na biya Naira Biliyan huɗu don magance wannan matsala,” inji shi.

 

Gwamnan ya bayyana irin matsalolin da ya gada, yana mai cewa: “Na samu asusun gwamnati da naira miliyan huɗu kacal. Ma’aikata suna karɓar albashi cikin rashin tabbas, babu ruwa, asibitoci kuwa suna cikin mummunan yanayi.”

 

Lawal ya ce, ya sake fasalin tsarin gwamnati, inda ya rage yawan kwamishinoni da manyan sakatarorin don rage ɓarna da ƙara inganci. “Yanzu muna daga cikin jihohi mafi ci gaba wajen tara haraji, inda kuɗaɗen shiga suka ƙaru da fiye da kaso 300 cikin 100,” inji shi.

 

Ya bayyana cewa gwamnatin sa ta gina ko ta gyara makarantu sama da 500, tare da aiwatar da ayyukan da kuɗinsu ya kai biliyan N10 a kowace ƙaramar hukuma. Duk da cewa ana cire biliyan 1.2 a kowane wata daga kuɗaɗen gwamnati don biyan basussuka, an biya bashin fansho da giratuti na fiye da biliyan N13.6 da aka tara tun shekarar 2011.

 

A ɓangaren tsaro, Lawal ya ce jihar ta ɗan sami sauƙi bayan kafa rundunar tsaron gida, yayin da gwamnati ke ƙoƙarin tabbatar da amfanin mulki ya kai ga talaka.

 

A nasa jawabin, Babban Editan LEADERSHIP, Azu Ishiekwene, ya ce an bai wa gwamnan wannan lambar yabo ne saboda irin nasarorin da ya samu a fannonin tsaro, ilimi, lafiya da gine-gine, yana mai cewa “jarida tana da alhakin duba gwamnati, amma kuma tana da haƙƙin yabawa idan ana yin daidai.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sanata Barau Zai Yi Ƙarar Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10 November 8, 2025 Labarai Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta November 8, 2025 Manyan Labarai Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja November 8, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
  • Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal
  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  • Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu!
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki