Aminiya:
2025-11-08@13:47:52 GMT

Jami’ar European-American ta musanta bai wa Rarara digirin girmamawa

Published: 21st, September 2025 GMT

Jami’ar European American University ta musanta bai wa fitaccen mawaƙin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara, digirin girmamawa na dokta.

A jiya Asabar ce dai wani bidiyo da ya karaɗe dandalan sada zumunta ya nuna yadda ake karrama Rarara da digirin girmamawa a wani bikin yaye ɗalibai da aka gudanar a otel ɗin NICON Luxury da ke Abuja.

Mutum 9 sun rasu a hatsarin jirgin ruwa a Sakkwato NAF ta hallaka Boko Haram 32 a Borno

Sai dai cikin wani saƙo da ta fitar a shafinta a ranar Asabar, jami’ar ta ce sam ba ta da hannu a lamarin kuma ba da izininta ba.

Jami’ar ta bayyana cewa, ba ta taɓa ba da izinin gudanar da taron karramawa ko taron yaye ɗalibai a wannan wurin da kuma wannan ranar ba.

Sanarwar ta ƙara da cewa, an shirya taron ne ta hanyar yaudara, ba tare da sanin jami’ar ba kuma ba tare da amincewarta ba.

Haka kuma, ta ce waɗanda suka shirya taron, sun yaudari jama’a “da nuna kamar suna wakiltar Jami’ar European-American.

“Wannan kuwa ƙarya ce tsagwaronta, domin ba su da wata alfarma ko izini, balle kuma su karɓi kuɗi a madadin jami’ar.

Jami’ar European-American ta ƙara da cewa, “ba ta taɓa bai wa Dauda Kahutu Rarara, Alhaji Ahmed Saleh Jnr., Mustapha Abdullahi Bujawa ko Tarela Boroh wata girmamawar digirin Doktora ba.

“Dukkan waɗanda jami’ar ta karrama da digiri na gaskiya suna cikin rajistar dalibai da aka yaye wacce ake iya dubawa a hukumance.”

Tun bayan ɓullar labarin digirin girmamawa da aka yi wa fitaccen mawaƙin siyasar, mutane da dama suke tofa albarkacin bakinsu, inda da dama suka taya shi murna, a ɓangare guda kuma wasu suka ƙalubanci lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dauda Kahutu Rarara Digirin Girmamawa Jami ar European American digirin girmamawa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

Majalisar Dattawa a ranar Laraba ta amince da kudirin da ke kayyade hukuncin daurin shekaru 14 ga malamai da aka samu da laifin cin zarafin dalibai mata a manyan makarantu. Wannan matakin ya zo ne a daidai lokacin da rahotanni ke ci gaba da cewa, malamai suna amfani da damar dalibai masu neman maki ko wata alfarma sai su yi lalata da su – wannan matsalar ta tabbata a wani bincike da aka yi a jami’o’in Nijeriya tsawon shekaru, ciki har da binciken sirri na 2019 mai taken “Lalata don samun maki”, wanda ya fallasa cin zarafin da ake yi a wasu jami’o’i. Dokar mai taken ‘Dokar Cin Zarafin Dalibai ta 2025’ (HB.1597), Sanata Opeyemi Bamidele (APC, Ekiti ta tsakiya) ne ya gabatar da ita domin amincewa. Bamidele ya bayyana cewa, an gabatar da kudirin ne don kare dalibai daga duk wani nau’in cin zarafin jima’i da cin zarafi a rayuwar makaranta, wadda ta tanadi dokokin shari’a don aiwatar da hukunci da hukunta masu laifi. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa November 5, 2025 Labarai Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu November 5, 2025 Labarai Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai November 5, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
  • Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya
  • Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i
  • Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Don Yaki da Laifuffuka A Maiduguri
  • Zulum ya bai wa hukumomin tsaro kyautar motoci 63 don inganta tsaro a Borno