Wannan yana faruwa sosai gaskiya, kuma ƙarshe ba a wayewa da lafiya gaskiya. Masu yi gaskiya tun wuri su daina wallahi, dan aure ya sha mutuwa ta sanadin haka ƙarshe azo ana nadama mara amfani. Sosai ana samun gagarumar matsala tsakanin ma’aurata zargi ya shiga tsakani, daga nan ma dai wani aure ka ji ya mutu.

Su yi wa kansu faɗa, su daina gaskiya.

 

Sunana Haj. Maryama Ahmad, daga Jihar Kaduna:

Wannan matsaloli suna faruwa sosai, kuma rashin tunani ne yake janyo hakan. Dalili kuwa ko da namiji ba shi da wannan tunanin na soyayya da wata to, kin ƙirƙirar masa ke da kanka, kin riga da kin nemo masa hanyar da zai riƙa samun damar bibiyar wasu. Haka lambar da za ki ara ko da ace ita macen ba ta bibiye shi ba, watarana zai ji yana son bibiyar lambar musamman lokacin da ki ka ɓata masa, sharrin ɗa namiji na da yawa ya san hanyoyin da dama waɗanda zai bi ya tursasa ita wannan me lambar ko da kuwa ba ta buƙatar sauraronshi har sai ya cimma burinshi. Kin ga kenan kin kawo wa kanki da kanki wata masifar kuna zaune lafiya ke da mijinki, Allah dai ya kyauta. Wannan darasi ne babba musamman ga ƴ an’uwa mata manya da yara, dan wata babbar kamar ƙaramar yarinya haka take. Allah ya sa mu dace.

 

Sunana Fadila Lamiɗo daga Jihar Kaduna:

In ban da ganganci akan wani dalili za ki ɗauki ‘number’ mijinki ki saka a wayar wata? wannan tamkar bawa mage ajiyar kifi ne, idan ma kina tunanin kin goge ‘number’ bayan kin gama ne shi mijin naki yau da gobe kina masa haka zai iya bin bayan ‘number’ don shi ba walliyi bane, garin neman gira sai a rasa ido. Ina kira ga mata su guji tsananta buncike, su sa a zuciyarsu kishiya ƙaddara ce kuma bawa baya iya gujewa ƙaddararsa. Su mayar da hankali wajen roƙon Allah abin da suke so wa kan su na alheri, in sha Allahu Allah zai shiga cikin lamarinsu, ba tare da sun ɗaga wa kansu hankali ba, wajen binciko abin da ka iya kawo masu rashin kwanciyar hankali.

 

Sunana Princess Fatimah Mazadu, daga Jihar Gomben Nigeria:

Tirƙashi kin san wauta da dolanci wallahi wannan shi ne, kat! ah to, in ba wauta ba ke kin isa ki gama sanin ɗa namiji? Ko chat da neman hanyoyi ta zamani za ta isar miki ki gane halayen mijinki ko sanin ƴ an matanshi ko neman aurenshi da makamantansu?. Ai tonon asiri ne da rashin sanin zafin kai, da ƙoƙarin saka zargi tsakanin zamantakewarku. Ai kira da babbar murya in har akwai masu niyyya ma wallahi kar su kuskura, dan wata in ta yi ta wanye lafiya, wata gidansu za a korata. Shurme ne sosai ace wai mace tana bibiyar namiji akan dole ta san ainihin abun da ke tafiya a rayuwarshi, an ce mana mazan daƙiƙai ne? ai sun fi mu wayewa a wannan fannin. Tunda dai ban taɓa jin an ce ga mace ta ƙirƙiri Tiktok ko Facebook ko Instagram ba, kawai ki kasance mai yadda da shi akowani hali idan bai saɓawa addininmu. Matsaloli kam, ai ba adadi dan garin gwadashi wallahi za ki gwado bala’i a ƙoƙarinki na ki san meke tafiya, kawai ana cikin hira ya ce misali “yau ina komawa ma zan saki matata tun da zan mallakeki…” Dan Allah ya za ki yi?  Shin za ki tonawa kanki asiri ne, ko za ki cigaba da chat ɗin?,  ko daga ya dawo za ki tare shi?, ko za ki hau haɗa kayanki ne?, kin ga wannan ƙaramin misali ne, wallahi mata su kiyayye wannan shurme ne. Matsaloli kamar; rashin kwanciyar hankali, zargin juna, nadama, da-na-sani, banzar aƙida.

 

Sunana Lawan Isma’il (Lisary), Rano LGA Jihar Kano:

Idan za a yi ba mai zurfi ba, kuma za a yi gwajin da zuciya ɗaya bada niyyar tayar da fitina ba a nawa fahimtar babu matsala. Akwaisu matsaloli kam, idan har ita cen ta fiye gwajin mai zurfi. Shawarata a nan ita ce, kawai duk wata mace tana yi wa mijinta kyakykyawan zato musamman akan ƙarin aure, domin Allah ne da kansa ya halastawa namiji ya auri mace har guda huɗu amma fa idan zai yi adalci, shi kuma adalci ubangijinmu ne kaɗai mai yinsa daidai. Allah kasa mu dace amin.

 

Sunana Hadiza Ibrahim D. Auta, Ɗaura-Namoda Jihar Zamfara:

Babban ƙalubale ne ga mata masu irin wannan halin bin diddigi, ko ga namiji ballantana ga mace wadda ba ta isa ta saka ko ta hana ba. Kira na ga masu irin wannan halin su daina gwajin su tsayar da hankalinsu a kan abin da suka gani zahiri. Saboda Allah da kansa ma ya ce kada mu tsananta bincike, gudun garin tone-tone kaza ta tono wuƙar yanka ta. Akwai illoli masu tarin yawa dangane da matsalolin da wannan gwajin yake haifarwa ga masu riƙo da shi a matsayin wayewa, ko babban makamin da suke riƙo da shi domin tabbatar ko gano; ana son su ko ba a son su, kuma mijinsu yana kula wasu matan ko babu ruwansa da su. Saboda ba a gwada namiji da mace komai muninta. Don akwai wata da ta taɓa saka ƙawarta ta yi wa saurayinta gwajin; daga haka aure ya ƙullu a tsakaninsu ya bar budurwarsa ta asali ya auri ƙawarta. Haka ma ƙawa ta taɓa kwace mijin ƙawarta a irin wannan gwajin daga wasa. Shawarata ga masu yi kawai su daina, a wannan zamanin da muke ciki miji ko saurayi duka ɓoye su ake yi kamar an samu kuɗi. Wata ko ba a saka ta yin gwajin ba gaban kanta take yi, idan ta samu dama sai dai ƙawar ta ji labari a sama zancen ya sauya, mai son ta ya koma kan ƙawarta ko kuma ƙawarta za ta aure mata miji.

 

Sunana Muktari Sabo, Jahun A Jihar Jigawa:

Mata mutanenmu lallai hakan tana faruwa wato mace take bibiyar mijinta ta hanyoyi mabambanta ciki kuma har ta waya. Kiran da zan yi akan haka shi ne, mata su ji tsoron Allah kuma su sani bibiyar ba abin da za ta hana wanda Allah ya sa zai faru. Akwai matsaloli; na farko dai ta ɗorawa kanta rashin kwanciyar hankali, sannan hakan zai iya haifar mata matsala tsakaninta da mijinta. Shawara a nan ita ce mata masu wannan hali su daina, domin yin hakan ba zai hana ayi musu abin da suke tsoro ba wato kishiya.

 

Sunana Hafsat Sa’eed, daga Jihar Neja:

A nawa tunanin hakan bai kamata ba, mace ta gwada kiran mijinta matsayin wata daban, duk abin da ya je ya zo kuwa ita ta jaho. Dan wannan kowaye ya ji ya san dole a samu matsala a gaba, kuma abin da macen ke tsoro za ta iya janyo shi da kanta. Idan ma zargi take kan yana aikata wani abun, sai ta barshi shi da ubangijinsa ya fi mata.

 

Sunana Hauwa Abubakar Sarki, daga Suleja Jihar Neja:

Kishi na iya sa mace ta aikata komai, duk yadda mace ta kai ga bin diddigin mijinta da sanya ido akan al’muransa, wai dan saboda kada ya ƙara aure yayyo mata kishiya wallahi aikin banza ne. Idan mijinki ya yi niyyar aikata abu musamman ƙara aure kuma bai yi niyyar gaya maki ba duk buncikenki ba za ki taɓa ganewa ba. Kiran da zan yi a gare su shi ne su bari, duk abin ki, baki isa ki hana namiji abun da yayi niyya ba. Musamman akan ƙarin aure, addu’a da miƙa al’amura zuwa ga Allah shi ne kaɗai mafita a gare mu. Sosai kuwa, illah ta farko shi ne, idan har ki ka kamasa da abin da ki ke zargin yana aikatawa babu abun da zai haifar maki sai tashin hankali. Shawarar da zan basu shi ne, idan har ba saɓon Allah yake da wanda yake neman ba  mafi a’ala shi ne ki bi shi da fatan alkhairi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Taskira

এছাড়াও পড়ুন:

Wata Mahanga Ta Daban Ta Kallon Ayyukan Ta’addanci

 

Al’amari mai rikitarwa

Hakikanin gaskiya ya fi an rikitarwa. Bisa al’amari, ana kiyasta cewa mutane kimanin 15,000 zuwa 20,000 ne suka mutu a sakamakon kashe-kashen da suka shafi ƴ an bindiga da ta’addanci a Arewa maso Yamma kaai cikin shekaru 10 da suka wuce. Wannan adadi yana daidai da yawan rayukan da aka rasa a Yakin Kosobo, ko kusan kashi 40 cikin ari na asarar rayuka a Yakin Basasar Saliyo na tsawon shekaru 10, duk da cewa ba gwamnati ba bace ke yakar ƴ an bindiga, sai dai ƴ an ta’adda ne masu zaman kansu.

Wannan kididdigar ba ta bayyana irin wahalar da dubban yara ke sha ba, waanda aka kashe iyayensu, gidaje marasa uwa ko masoya, mutane da suka ji rauni har abada ko aka raba su da muhallansu, hanyoyin neman rayuwa da aka lalata, makoma da aka rusa, da rayuwar yanzu da ake yi cikin tsoro da rashin tabbas.

Lawal ya taba ba da labari kan yadda wasu ƴ an bindiga, waanda aka gano shirinsu bisa bayanan sirri, suka tsere kafin ya iya ratsa dogon jerin umarnin soja na Abuja.

Yana da, domin yana takaicin yadda ake rage karfin gwamnoni tare da mai da su tamkar wasu jagorori ta fuskar manyan matsalolin tsaro, domin muna shakku akansu cewa za su iya yin amfani da rundunar ƴ an sandan jihohi wajen zalunci.

 

Ilimin Zamantakewar Ƴan Bindiga

Sai dai, ba fasaha da ƴ ansandan jihohi kaai ne za su iya takaita wannan masiba ba. Wannan shi ne abin da wani bincike da Cibiyar Nazarin Harkokin Kasa ta Denmark ta gudanar a Agustan 2025. Sakamakon binciken, wanda aka saki kwanan nan, ya cancanci a yi la’akari da shi.

Binciken da Peer Schouten da Barnett James suka gudanar na farko, babban mai bincike na biyun kuma alibin PhD a Jami’ar Oford, mai taken “Dibided, They Rule? Sabon Yanayin Ƴan Bindiga a Arewacin maso Yammacin Nijeriya

“Binciken ya duba ilimin zamantakewar ƴ an bindiga, tushensu da yadda suka samo asali, da kuma yadda suka maye gurbin ƴ an jihadi waanda a da suka fi rinjaye a matsayin reshen Sahel mai girman tasiri.

Labari na yau da kullum kan ƴ an bindiga, ƴ an jihadi, da masu tsattsauran ra’ayin addini ya kan bayyana su a matsayin “ƴ an ta’adda da masu laifi.” Sai dai wannan bincike ya auki wata hanya mai zurfi wadda ta bayar da wata fahimta, inda ya bambanta ƴ an bindiga da ƴ an jihadi ko wasu kungiyoyin laifi, musamman bisa akida, wuri, da kuma hanyoyin gudanar da ayyuka.

Ya ce, alal misali, “Sabani da kungiyoyin jihadi, kungiyoyin ƴ an bindiga ba sa aiki bisa ga wata akida ta ra’ayi, amma suna da tasiri sosai a mulkin yankunan karkara, suna kalubalantar ikon gwamnati ta hanyar fyae da yin barna, da kuma ta hanyar tsayayyen haraji da karbar kuin fansa.”

 

Lallai Lamarin Ta’addanci Ne

Sau da yawa na kan yi amfani da kalmomin nan ba tare da bambanci ba. Amma su idan suna magana suna banbancewa, kamar su ce, ƴ an bindiga suna kai hari, masu garkuwa na kai hari, kuma dukkansu suna barin jama’a cikin bakin ciki, hawaye da jini, to, a wajena dukkan su ƴ an bindiga ne, ƴ an jihadi, ƴ an ta’adda da masu laifi. Sai dai manufar binciken ita ce, idan ba a tantance dalilai da hanyoyin da suke bi ba, to mayar da martani da manufofi na iya sauka daga ainihin layin da ya dace.

Idan za mu yi magana da salon Lawal, Gwamnan Zamfara ko duk wani gwamna a Arewacin maso Yammacin Nijeriya da ke sha’awar shawo kan matsalar tsaro, domin ya yi aiki fiye da ikon zartarwarsa don ya yi nasara, to ba ya ga samun ƴ ansandan jiha, dole ne su fahimci ilimin zamantakewa da tunanin abokan gaba, in ba haka ba, watakila mu shiga mawuyacin hali fiye da yanzu a cikin watanni arba’in.

Wannan binciken ya bayyana yadda, ta hanyar tsarin “yin barna da kuma kararbar kuin fansa,” Tun daga shekarar 2011 ƴ an bindiga suka kirkiro wani tsarin mulki “wanda hanyoyi ne masu muhimmanci da suke tunatar da tsarin mulki na tattara haraji a yankin tun kafin zuwan Turawan mulkin mallaka.”

 

Yekuwa Daga Daular Usmaniyya

A cikin tausasa harshe, binciken yake cewa ƴ an bindiga, waanda suka samo asali kusan shekaru 15 da suka gabata, suna maimaita wani fasali na tsarin Khalifanci a Arewacin Nijeriya, wanda ya dogara kan “kai hari da karbar haraji” don faaawa da kuma tabbatar da wanzuwar tsarin.

A cewar binciken, “Ƴan bindiga na yau,” “suna maimaita waannan tsarin, inda babura na zamani da wayoyin hannu suka maye gurbin dawaki da bindigogin karni na 19.

Duk da cewa kayan aikin sun canza ba kamar na da ba, amma tsarin mulki da tattara arziki na asali suna nan kamar yadda suke, wanda hakan yana da matukar wahala mutanen karkara da wasu waanda abin ya shafa su fahimta.”

Binciken bai auka cewa duk ƴ an bindiga Fulani ne ba, kamar yadda aka fi samu a karni na 18 da na 19. Ko kuma cewa suna da burin gina jiha ko tsantsar imani kamar ƴ an jihadi na lokacin. Sai dai, binciken ya lura da maimaita wasu tsarin iko da sahihanci a waannan yankuna da suka yi kama da tsarin Khalifanci.

 

Lamarin Ya Zama Gagaradau

Lawal ya ji takaici kan rasa babban burinsa akan kawo karshen ƴ an bindiga saboda tsarin umarni na soja. A bangaren su, sojoji ma sun kai hari kan fitattun shugabannin ƴ an bindiga, inda nasarorin baya-bayan nan suka haa da Baleri Fakai da Halilu Buzu.

Waannan matakai sun kasance gagarumin ci gaba a yaki da ƴ an bindiga. Sai dai, wannan binciken ya kwatanta kungiyar ƴ an bindiga da dabbobi wato (Hydra-headed monster). Kungiya ce mai hain gwiwa amma ba ta da tsari mai karfi, wadda ke iya daidaitawa da sake habaka kanta ko da an cire shugaba na yanzu.

An tsara su ne don su iya jure rashin shugabansu, inda cire su wani lokacin ba abin so bane ga al’ummar da suke ciki.

Me ya sa? A bara, lokacin da aka kashe Halilu Sububu, alal misali, wata majiya ta shaida wa masu binciken cewa, “Kuskure ne a kashe Buzu (Halilu). Ya fara yin abubuwa masu kyau, yana gaya wa ƴ an bindiga su daina damun Fulani, wanda hakan yi tasiri soasi a Zamfara, Kaduna, Katsina, Kebbi da Sokoto.”

A wasu kalmomi, a wani yanayi na canjin hali mai ban mamaki, ƴ an bindiga suna sauyawa daga “ƴ an ta’adda da masu laifi” zuwa “masu kula,” suna cike gibin da gwamnati marasa halarta suka bari.

Za ka iya kiran shi ‘Stockholm Syndrome’, idan ka so, amma waanda suka yi mamakin dalilin da ya sa shugaban ƴ an bindiga, Kachalla Ado Aliero, aka naa shi Sarkin Fulani a Zamfara a 2022, ba sai sun sake tambaya ba.

Kuma waanda suka ji haushi da rashin hankali wajen yin yarjejeniya da ƴ an bindiga maimakon tarwatsa su da bama-bamai, watakila za su so su dakata su yi tunani akan dalilin yin hakan.

Yayin da ya kawo wani misali a cikin wani lamari mai tausayi, binciken ya ce, “A shekarar 2024, mutanen Kachalla Najaja (ƴ an bindiga) sun hukunta garin Anka (a Zamfara) saboda karbar masu gadi na gari ta hanyar hana mazauna garin girbin dawa, suna amfani da yunwa a matsayin hanya don tilasta su yin biyayya.”

A karshe, mazauna garin da suka shiga cikin hali na tsanani sun cimma yarjejeniya ta “zaman lafiya” ta hanyar biyan Naira miliyan 50. Wani mai shiga tattaunawar ya bayyana cew, ‘Shugabanmu na gida ya hana mu shiga sulhu, amma ba zai iya ba mu kariya ba ko ya samar mana da abin da za mu ci.”

 

Su karbi kui masu yawa, su mutu da talauci

Me ƴ an bindiga ke yi da kuin? Suna ajiye “dukiyarsu,” mafi yawanci daga haraji na tilas, kuin fansa ne, da satar shanu, a cikin sifofi masu saukin sarrafawa, wanda suke amfani da su wajen sayen karin shanu, sannan kuma a wajen sayen makamai alamari ne mai muhimmanci.

Kamar yadda manyan masu mallakar bayi a Afirka lokacin mulkin mallaka suka kasance, darajar shugabannin ƴ an bindiga wani lokaci ana auna ta ne da adadin mayaka, waanda aka sace ko mabiyansu, ba sa yin karyar nuna daidaito, domin shugaban yana more wani kaso na dukiyar da aka sato.

Sai dai, duk da shahararsu ta almara, wani masunci daga Kebbi ya shaida wa masu binciken cewa, “Kaan ne abin da suke samu na duniya” kuma suna mutuwa cikin talauci.

Binciken ya kawo karshe cewa ƴ an bindiga suna ta’addanci ne sakamakon rashin jajircewa mai orewa wajen raya karkara, samar da damammakin tattalin arziki, da kuma gyaran cibiyoyi. Wannan abu ne da mai hankali ya dace ya yi tunani a kansa ga kowace gwamnati da ke sha’awar warware wannan matsala nan ta tsawon lokaci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Groosi: Masu Binciken Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Suna Hanyar Zuwa Iran
  • Kasar Sin Za Ta Shirya Taron Mata Na Duniya A Beijing Yayin Cika Shekaru 30 Da Taron Mata Na 1995
  • Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu
  • APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027
  • Mata 400 sun amfana da kayan haihuwa a Gombe
  • Mata Ne Ƙashin Bayan Gyaran Duk Wata Al’umma, In Ji  Sheik Shamsudeen
  • Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja
  • Wata Mahanga Ta Daban Ta Kallon Ayyukan Ta’addanci