Aminiya:
2025-11-08@15:15:21 GMT

An yi garkuwa da ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

Published: 23rd, September 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato, mai wakiltar Mazaɓar Pankshin ta Kudu, Laven Denty Jacob.

A yammacin ranar Litinin aka yi garkuwa da shia gidansa da ke Anguwan Kagji, a Unguwar Dong, a Ƙaramar hukumar Jos ta Arewa.

Wani na kusa da shi ya tabbatar wa manema labarai cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 7:30.

A cewar mai taimaka wa ɗan majalisar, wasu mutane uku ne, da suka rufe fuskokinsu suka kai hari a ƙofar gidansa, a lokacin da suke jiran jami’an tsaronsa su buɗe kofar.

Ya bayyana cewa maharan sun ɗauke ɗan majalisar da ƙarfi daga cikin motarsa zuwa wani wuri, da ba a sani ba.

Ya ce masu garkuwar sun buqaci iyalansa su a biya su, kuɗin fansa naira miliyan hamsin.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred da Shugabannin Majalisar Jihar, har yanzu ba su ce komai ba, kan wannan al’amari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ɗan majalisar Garkuwa Majalisar Dokokin Jihar Filato

এছাড়াও পড়ুন:

Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa

Daga Usman Muhammad Zaria

Gidauniyar Tunawa da Marigayi Sir Ahmadu Bello (ABMF) ta yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa sauƙin kai, tawali’u da jajircewarsa wajen ci gaban Jihar Jigawa.

Shugaban Kwamitin Amintattu na Gidauniyar kuma tsohon Gwamnan Jihar Neja, Dr. Mu’azu Babangida Aliyu ne ya yi wannan yabon yayin da ya jagoranci tawaga zuwa gaisuwar ban girma a fadar gwamnatin jihar da ke Dutse.

Ya ce salon jagoranci na Gwamna Namadi na ɗauke da ƙima da marigayi Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato, ya shahara da su, musamman tsari, girmama jama’a da shugabanci na gaskiya da rikon amana.

Dr. Aliyu ya yi kira ga shugabannin Arewa su rungumi jagoranci da ke maida hankali kan al’umma, tare da fifita ilimi a matsayin tubalin cigaba.

Ya kuma sanar da cewa Jihar Jigawa ce za ta karbi bakuncin taron gidauniyar na shekarar 2026, wanda zai ƙunshi laccoci, shirye-shiryen wayar da kan jama’a da bada lambar yabo.

A jawabinsa, Gwamna Namadi ya gode wa Gidauniyar bisa wannan yabo da kuma zaɓar Jigawa don karɓar taron na 2026.

Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da bin sawun Sardauna ta hanyar shugabanci na gaskiya, tsare-tsaren jin daɗin jama’a da kuma zuba jari a fannin ilimi.

Ya tabbatar da cikakken goyon baya wajen shirya taron 2026 cikin nasara.

Tawagar ta haɗa da Madakin Zazzau, Malam Muhammad Munir Ja’afaru, da wasu jami’an Gidauniyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  • Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah
  • Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu
  • Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu
  • Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai
  • Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu