Aminiya:
2025-11-08@15:48:21 GMT

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙara haɓaka — NBS

Published: 22nd, September 2025 GMT

Hukumar Ƙididdigar a Najeriya, NBS ta ce arzikin cikin gida da ƙasar ke samu ya ƙaru da kashi 4.23 cikin 100 a rubu’i na biyu na shekarar 2025 da muke ciki.

Sabbin alƙaluman da hukumar ta fitar sun nuna cewa an samu ƙarin kashi 3.48, idan aka kwatanta da daidai wannan lokacin a 2024, lamarin da hukumar ta ce alamu ne na bunƙasar tattalin arzikin ƙasar.

An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya CAC ta soma yi wa kamfanoni rijista da fasahar AI

NBS ta ce fannin aikin gona ne kan gaba wajen samar da ƙaruwar arzikin ƙasar, wanda ya ƙaru zuwa kashi 2.82 saɓanin kashi 2.60 a 2024.

Sauran fannonin da hukumar ta ce an samu ci gaba sun hada da fannin masana’antu da, da man fetur da kuma fannin ma’adinai.

NBS ta ce a rubu’i na biyu na shekarar 2025, arzikin cikin gida da Najeriya ta samu ya kai naira tiriliyan 100.73, ƙari kan naira tiriliyan 84.48 da aka samu a 2024 daidai wannan lokacin, abin da ke nuna ƙarin kashi 19.23 cikin 100.

A watan jiya na Agusta ne Majalisar Ƙoli ta tattalin arziki a Najeriya, ta sanar da amincewa da sabon tsarin ci gaban tattalin arziki zango na biyu na tsawon shekaru 5 wato 2026-2030, bayan ƙarewar zangon farko wato daga 2021 zuwa 2025.

Sabon tsarin da majalisar ta ƙaddamar wadda ke ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shetima ci gaban tattalin arziki zai yi la’akari da sauye-sauyen da aka samu kamar cire tallafin man fetur, sabbin dokokin haraji da makamatansu.

Ƙarƙashin sabon tsari ne kuma gwamnatin ke son cimma ƙarfin tattalin arziƙi na Dala tiriliyan ɗaya nan da shekarar 2030, abinda ya dace da manufofin ƙasar har zuwa shekarar 2050.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tattalin Arziki

এছাড়াও পড়ুন:

An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8

An rantsar da Paul Biya a matsayin shugaban ƙasar Kamaru karo na takwas mai shekaru 93 a majalisar dokokin ƙasar da ke Yaoundé.

Paul Biya ya shafe shekaru 43 yana mulkin ƙasar, kuma yanzu zai fara wani wa’adi na tsawon shekara bakwai nan gaba.

Ƙungiyyar Ƙwallon yashi ta Kada BSC ta fatattaki Kebbi BSC Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa

Biya wanda shine shugaban ƙasa mafi tsufa a duniya, ya sami kashi 54 na ƙuri’un zaɓe, yayin da abokin takararsa, Issa Tchiroma Bakary ya samu kashi 35%, a cewar sakamakon zaɓen hukumar ƙasa.

Tchiroma Bakary dai ya yi iƙirarin cin nasara a zaɓen da aka yi yana kuma zargin cewa an yi maguɗin zabe, wanda hukumomi suka musanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Mun sami gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Yaduwar Juyin Mulki A Afirka
  • Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
  • Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho
  • An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8
  • Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka