Gazawar Shugaba Bola Tinibu Ne Ya Sa Sanata Marafa Ficewa Daga APC
Published: 20th, September 2025 GMT
Shugaban kungiyar goyon bayan Sanata Marafa, Alhaji Surajo Garba Maikatako, ya ce ficewar Sanata Kabir Garba Marafa daga jam’iyyar APC ya kara karfafa masa siyasa tare da jaddada goyon bayansa ga magoya bayansa.
A wata sanarwa mai dauke da sa hannun sa da kan sa, Alhaji Maikatako ya bayyana cewa Sanata Marafa ya yanke shawarar ficewa daga jam’iyyar APC ba wani yunkuri ne na kashin kai ba, sai dai an dauki matakin ne na gama-gari bayan tattaunawa da magoya bayan sa.
Ya ce tun bayan wannan sanarwar kungiyar ta fara samun sakonni da ziyarce-ziyarcen hadin kai daga fadin jihar Zamfara da Arewa maso Yamma da kuma wajenta, inda da yawa ke bayyana shirin tafiya da sabuwar alkiblar siyasa.
A cewarsa, wannan ci gaban alheri ne kuma ya zama wani sauyi a tafiyarsu ta siyasa.
Alhaji Surajo Garba Maikatako ya bayyana Sanata Marafa a matsayin daya daga cikin shugabanni masu kishin kasa kuma masu hangen nesa wadanda siyasarsu ta ginu akan adalci, rikon amana da yiwa al’umma hidima.
Alhaji Maikatako ya ci gaba da cewa, sabanin ikirari da shugabannin jam’iyyar APC na Zamfara ke yi, Sanata Marafa yana samun goyon bayan talakawa, inda ya ce har yanzu jam’iyyar ba ta lamunta da ficewar sa.
Ya yi zargin cewa jam’iyyar APC a Zamfara ta rasa nasaba da siyasa, inda ya nanata cewa, wadanda ake yi wa lakabi da wadanda za su maye gurbin Sanata Marafa ba su da ra’ayin jama’a kuma ba za su iya gabatar da zaben jam’iyyar nan gaba ba.
Shugaban kungiyar ya kuma alakanta ficewar Sanata Marafa da gazawar shugaban kasa Bola Tinubu wajen cika alkawuran yakin neman zabe, musamman kan rashin tsaro a jihar Zamfara, duk kuwa da rawar da Sanatan ke takawa a matsayin kodinetan yakin neman zaben jihar a zaben 2023.
Ya kuma jaddada cewa kungiyar tasu a yanzu tana shirye-shiryen wani abin da ya bayyana a matsayin yakin neman zaben shugaban kasa mai cike da tarihi, inda ya bukaci magoya bayansa da ‘yan Najeriya masu kishin kasa da su hada kai wajen kwato mulkin dimokaradiyya da dawo da martabar mulki.
REL/AMINU DALHATU.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Marafa Zamfara jam iyyar APC Sanata Marafa
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m
Wani ɗan kasuwa a Jihar Katsina mai suna Anas Ahmadu da matarsa, Halimatu wadda ke ɗauke da juna biyu, da kuma ’yarsu mai shekaru biyu, sun kuɓuta daga hannun ’yan bindiga, bayan sun shafe kwanaki 21 a hannunsu.
An sako su ne a daren ranar Laraba bayan biyan kuɗin fansa Naira miliyan 50, kamar yadda wani ɗan uwansu ya bayyana wa Aminiya.
Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas NAJERIYA A YAU: Wadanne Kalubale Gwamna Fubara Zai Fuskanta Bayan Dawowa Mulkin Ribas?“Alhamdulillah! Anas, Halimatu da ’yarsu sun kuɓuta. Yanzu haka suna kan hanyarsu ta zuwa gida, amma sai da aka biya ’yan bindigar kuɗin fansa Naira miliyan 50,” in ji shi.
An sace su ne a ranar 26 ga watan Agusta, 2025 a gidansu da ke Filin Canada Quarters, a Jihar Katsina.
Da farko, mahafan sun nemi Naira miliyan 600, daga baya suka rage kuɗin zuwa miliyan 100, sannan daga ƙarshe suka amince aka biya su miliyan 50.
Saboda dalilan tsaro, ’yan uwansu ba su bayyana inda aka sako su ba.