Aminiya:
2025-11-08@14:37:29 GMT

Mata 400 sun amfana da kayan haihuwa a Gombe

Published: 21st, September 2025 GMT

Ƙaramar Hukumar Gombe, ta raba wa mata masu juna guda 400 kayan haihuwa kyauta, domin kare lafiyarsu da rage mace-mace a yankin.

An gudanar da rabon ne a Cibiyar Haihuwa ta Gombe a ranar Alhamis, inda shugaban Ƙaramar Hukumar, Barista Sani Ahmad Haruna, ya jagoranci rabon.

Hatsarin mota ya yi ajalin mutum 4, 16 sun jikkata a Yobe Gwamnan Gombe ya bai wa maharba kyautar motoci da babura don bunƙasa tsaro

Shugaban ya ce shirin ya yi daidai da umarnin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, na bunƙasa kiwon lafiya a matakin farko, musamman ga mata masu juna biyu daga lokacin ɗaukar ciki har zuwa haihuwa.

Ya kuma bayyana cewa an fara gwajin jini kyauta ga mata masu juna biyu a dukkanin cibiyoyin haihuwa, domin gano matsalolin lafiya tun da wuri.

Wasu daga cikin matan da suka amfana sun gode wa gwamnati, inda suka bayyana cewa shirin zai rage musu kashe kuɗi tare da tabbatar da lafiyarsu da ta jariransu.

Wata mata mai suna Sa’adatu Garba, ta bayyana jin daɗinta game rabon kayan.

“Wannan kaya da aka ba mu tabbas za su taimaka, musamman duba da halin matsi da ake ciki,” in ji ta.

Ita kuwa Rabi Mustapha cewa ta yi: “Wannan babban tagomashi ne, muna godiya Allah Ya saka da alheri. Wannan shiri zai sauƙaƙa mana wajen rage kashe kuɗaɗe.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ƙaramar Hukumar Gombe lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Masu Sa Ido na Tarayyar Afirka: Zaben Tanzania Ya Keta Ka’idojin Demokradiyya

Tawagar masu sa ido ta Tarayyar Afirka ta sanar a ranar Laraba cewa zaɓen Tanzania “bai cika ƙa’idodin dimokraɗiyya ba,” tana mai tsokaci kan zaɓen da aka yi jayayya a kansa wanda ya haifar da zanga-zanga mai tsanani kwanan nan.

An ayyana Shugaba Samia Suluhu Hassan a matsayin wadda ta lashe zaɓen da gagarumin rinjaye a zaɓen da aka gudanar a ranar 29 ga Oktoba, amma ‘yan adawa sun zargi gwamnati da yin magudi a zaɓen, kuma zanga-zangar ta ɓarke ​​bayan da aka soke manyan abokan hamayyarta.

Tawagar ta ƙara da cewa “a wannan matakin farko, tawagar ta kammala da cewa babban zaɓen 2025 a Tanzania bai yi daidai da ƙa’idodin Tarayyar Afirka da tsarin ƙa’idoji na kasa da kasa  da kuma sauran alkawuran ƙasa da ƙasa na zaɓen dimokraɗiyya ba.”

Ta ƙara da cewa “masu sa ido sun lura da cunkoson jama’a a akwatuna a rumfunan zaɓe da dama, inda aka raba ƙuri’u da yawa,” sannan ta lura da “rashin wakilcin sauran  jam’iyyun siyasa, haka nan  kuma a lokacin ƙidayar ƙuri’a, an nemi wasu masu sa ido su bar rumfunan zaɓe.

Tawagar ta kara da cewa “Dole ne Tanzania ta ba da fifiko ga gyare-gyaren zaɓe da na siyasa don magance ƙalubalen dimokuraɗiyya a kasar.

A nata ɓangaren, gwamnati ta dage a kan cewa zaɓen ya gudane a cikin aminci da sahihanci da gaskiya.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Kama ‘Yan Jarida 3 A Nijar Bisa Tuhumar  Fitar Da Bayanai Na Hukuma November 5, 2025 Sudan Ta Sake Jaddada Tuhumar Kasar UAE  Da Taimakon Rundunar RSF November 5, 2025 Shugaban Mali Ya Yi jawabi Akan Hana Shigar Da Man Futur Da Masu Ikirarin  Jihadi Suke Yi November 5, 2025 Iran : bisa sharadi ne muka saki ‘yan Faransa daga gidan yari November 5, 2025 Gaza : MDD Ta damu kan keta yarjejeniya tsagaita wuta da Isra’ila ke yi  November 5, 2025 Kungiyoyin agaji sun ce tallafin da ake bai wa Gaza bai isa ba November 5, 2025 China ta yi alkawarin ci gaba da tallafawa Najeriya bayan barazanar Trump November 5, 2025 Imam Khamenei: Rikici Tsakanin Iran da Amurka na asasi ne November 5, 2025 Iravani: Kalaman Trump barazana ne ga zaman lafiyar duniya November 5, 2025 Khatibzadeh: Shirin Nukiliyar Iran ne aka fi maganarsa a duniya November 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  • An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani
  • Masu Sa Ido na Tarayyar Afirka: Zaben Tanzania Ya Keta Ka’idojin Demokradiyya
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
  • Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i
  • Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 
  • Likitoci sun wayar da kan mata kan cutar Sankara a Gombe