Kasar Sin Na Son Karfafa Hadin Gwiwar Masana’antu Da Dukkan Bangarori
Published: 21st, September 2025 GMT
Babban mai ba da shawara kan harkokin siyasa na kasar Sin Wang Yong ya bayyana cewa, kasar Sin tana son karfafa hadin gwiwa da dukkan bangarori a muhimman fannoni kamar na masana’antu.
Wang, wanda shi ne mataimakin shugaban babban kwamitin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin, wacce take babbar hukumar ba da shawarwari kan harkokin siyasa ta kasar Sin, ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a wajen bikin bude taron masana’antun duniya na shekarar 2025 da aka gudanar a lardin Anhui da ke gabashin kasar Sin.
Wang ya kara da cewa, a cikin ‘yan shekarun da suka gabata, kasar Sin tare da dukkan bangarorin da abin ya shafa, sun bi ka’idar samun moriyar juna da hadin gwiwar samun nasara ga ko wane bangare, tare da yin amfani da dandalin taron wajen zurfafa hadin gwiwa a aikace, da ba da goyon baya mai karfi ga bunkasa masana’antun duniya.
Kazalika, Wang ya ce, a yayin da ake fuskantar wani sabon zagaye na juyin juya halin fagen kimiyya da fasaha da sauye-sauyen masana’antu, kasar Sin tana son yin aiki tare da dukkan bangarori don karfafa hadin gwiwa a muhimman fannoni kamar na masana’antu, da karya shingen da aka gitta a fannoni daban daban kamar na fasaha, da kaifin basira da harkar bayanai, da samun nasara a fasahohi masu muhimmanci, tare da cimma muradin samun ci gaba mara gurbata muhalli da rage fitar da hayaki mai gurbata yanayi. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen: ‘Yan Koren Amurka Da Isra’ila Suke Neman Wargaza Hadin Kan Larabawa Da Na Musulmi
Jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen ya jaddada cewa: ‘Yan koren Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila na da nufin wargaza hadin kan Larabawa da na Musulmi
Jagoran kungiyar Ansarullahi ta kasar Yemen Sayyed Abdulmalik al-Houthi ya jaddada cewa: ‘Yan koren Amurka da na haramtacciyar kasar Isra’ila suna neman tada fitina da sanya kiyayya a tsakanin al’ummomin Larabawa da na Musulmi. Ya yi nuni da cewa wadannan ‘yan kore ba su da wani aiki na gaske da zai yi hidima ga kasashensu na asali, sai dai mayar da hankali kan kokarinsu wajen wargaza zamantakewar al’umma, karkashin kulawar Amurka da tallafin Larabawa da kuma jagorancin yahudawan sahayoniyya.
A cikin jawabin da ya gabatar a jiya Lahadi, a daidai lokacin da ake gudanar da zagayowar ranar juyin juya halin Musulunci na ranar 21 ga watan Satumba, Sayyid Al-Houthi ya ce: Dukkan ayyukan makaman Amurka da na haramtacciyar kasar Isra’ila, da kafafen yada labaransu, an karkata sune zuwa ga tada fitina da kunna kiyayya, da tayar da zaune tsaye karkashin tutar bangaranci, sabanin mazhaba, yanki, da kabilanci.
Ya yi bayanin cewa, “‘Yan koren Amurka da hukumar leken asirin Isra’ila ba su da wani aiki na hakika na yi wa kasa hidima, don haka yunkurinsu ya dogara ne kan kunna wutar gaba, sabani da kuma kiyayya da ake nunawa a halin da ake ciki.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Gilla Kan Fararen Hula 5 A Kudancin Kasar Lebanon September 22, 2025 Ministan Harkokin Waken Falasdinu Ta Yi Kira Ga Karin Kasashe Su Amince Da Samuwar Kasarta September 21, 2025 Iran Da Pakistan Sun Sake Tsara Dangantakarsu Ta Tattalin Arziki September 21, 2025 Trump Ya Bukaci Afganistan Ta Mayarwa Amurka Sansanin Jiragen Sama Na bagram September 21, 2025 Kasashen Ingila Da Canada Da Kuma Australia Sun Bayyana Amincewarsu Da Samuwar Kasar Falasdinu September 21, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kira Ga Samar Da Tattalin Arziki Da Shugabancin Kwararru September 21, 2025 Arakci Ya Kore Cewa Ya Zanta Da Steven Witkoff Na Amurka September 21, 2025 Hizbullah Ta Yi Gayyar Tunawa Da Zagayowar Shahadar Sayyid Hassan Nasrallah September 21, 2025 Hamas Ta Yi Bukaci A Hukunta HKI Akan Rusa Asibitoci September 21, 2025 IRGC: Duk Wani Sabon Kuskuren Abokan Gaba Zai Fuskanci Mayar Da Martani Mai Tsanani September 21, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci