Wata mata ta ƙona farjin ’yarta da wuta kan zargin maita a Bauchi
Published: 19th, September 2025 GMT
Wata mata mazauniyar garin Magama Gumau a Ƙaramar Hukumar Toro, Jihar Bauchi, ta shiga hannun ’yan sanda biyo bayan ƙona farjin ’yarta mai shekaru 10 kacal a duniya, kan zargin maita.
Rahotanni sun nuna cewa matar ta yi amfani da cokali ta hanyar sanya shi a wuta ya yi zafi sannan ta umarci ’ya’yanta biyu suka riƙe yarinyar sannan ta ƙona ta.                
      
				
Wannan ya jefa yarinyar cikin mawuyacin hali, inda ta ke fama wahalar yin fitsari da bayan gida.
Bayan lamarin ya faru, maƙwabta sun kai ƙarar matar wajen ’yan sanda.
An garzaya da yarinyar zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) domin kula da ita.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Bauchi, CSP Mohammed Ahmed Wakil, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce an kama matar da wasu, ciki har da wata mai maganin gargajiya mai suna Fatima Abdullahi, wadda ta karɓi kuɗin matar sannan ta tabbatar mata cewa yarinyar mayya ce.
A cewar rundunar, lamarin ya faru ne ranar 11 ga watan Satumba, 2025.
Tuni Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike, tare da tabbatar da adalci.
’Yan sanda sun kuma ja hankalin iyaye da su daina kai yara wajen bokaye, domin hakan na iya jawo ɓarna maimakon samun waraka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Mayya zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Karuwanci da zubar da cikin ’yan mata ’yan gudun hijira ya karu a Maiduguri
Sarakunan gargajiya, lauyoyi da jami’an gwamnati sun koka bisa yawaitar kananan ’yan mata da ke daukar ciki da kuma zubar da ciki ba bisa ƙa’ida ba, a sansanonin ’yan gudun hijira da ke Maiduguri, Jihar Borno.
Lamarin ya fito fili ne a wani taron tattaunawa na kwanaki biyu da ƙungiyar Grassroots Researchers Association (GRA) ta shirya tare da tallafin We Are Not Weapons of War (WWoW) a karshen makon da ya gabata a Maiduguri.
Taron ya haɗa mutane fiye da 500, ciki har da waɗanda suka tsira daga fyade da cin zarafi a lokacin rikici, sarakunan gargajiya, lauyoyi, jami’an gwamnati da abokan ci gaban ƙasa, domin tattauna hanyoyin magance wannan matsala.
“’Yan mata kanana na sayar da jikinsu, suna kuma zubar da ciki a bandaki,” in ji wata mai taimaka wa GRA, Zaynab Abdallah.
NAJERIYA A YAU: Rashin aikin yi da hanyoyin magance su a Najeriya Gidan rediyo ya ɗauki nauyin sanya yara 40 a makaranta a KanoShugaban sansanin ’yan gudun hijira na EYN Jerusalem da ke unguwar Wulari a Maiduguri, Mista John Gwoma, ya bayyana yadda kananan ’yan mata da ƙananan yara ke fadawa tarkon lalata da kuma zubar da ciki a asirce.
Ya ce, “Wasu maza daga cikin gari kan zo cikin manyan motoci su ɗauki waɗannan ’yan mata ƙanana, su yi lalata da su har su sami ciki. Saboda haka yanzu zubar da ciki ba bisa ƙa’ida ba ya zama ruwan dare a sansanin.”
Ya ƙara da cewa, “Bandakunan mata sun koma kamar mayanka. Ana samun jini ko’ina saboda waɗannan ’yan matan na shiga su zubar da ciki sannan su bar tayin a ciki. Wasu iyaye na sane da abin da ’ya’yansu ke yi”
Wata mai taimaka wa GRA, Zaynab Abdallah, ta tabbatar da wannan zargi, tana mai cewa karuwanci da kuma zubar da ciki tsakanin ƙananan yara na ƙara yaduwa a Maiduguri.
Ta ce, “Wasu daga cikin waɗannan ’yan mata ƙanana suna lalata ne domin samun kuɗin abinci ga iyalansu. Amma abin takaici, wasu iyaye suna sane da hakan, amma suna yi shiru saboda suna amfana da abin da ’ya’yansu ke samu.”
Zaynab ta ci gaba da cewa, “Talauci ya kai ga karuwanci ya zama tamkar wani ɓangare na rayuwarsu. Ba za ka iya hana su ba. Idan sun sami ciki, sai su zubar da shi a ɓoye domin guje wa tozarci.”
Rikici da talauci sun kai mata ga lalacewa”A yayin zaman, waɗanda suka tsira daga fyade da sauran masu ruwa da tsaki sun ruwaito irin raɗaɗin da suka sha na fyade, da kuma yadda matsin tattalin arziki ke tura mata cikin harkar karuwanci.
Sai dai sun kuma bayyana yadda gangamin wayar da kai na GRA ya taimaka wajen rage tozarci da suka sha, tare da ƙara musu ƙarfin guiwa wajen neman adalci a kotuna.
Daraktan gudanarwa na ƙungiyar GRA, Mista Friday Bitrus, ya ce sakamakon tattaunawar da suka samu daga mahalarta zai zama ginshiƙi wajen fitar da takardar “Kira ga Daukar Mataki” domin tursasa gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki su ɗauki matakai na gaskiya.
Ya ce, “Abin da muka tattara daga bakin waɗanda abin ya shafa da sauran mahalarta ya nuna cewa akwai gaggawar buƙatar tsari na musamman don kare ’yan mata da mata daga fyade, ciki da kuma zubar da ciki a sansanonin.”
Kira ga gwamnatiMasu ruwa da tsaki a taron sun yi kira ga gwamnati ta ƙara tsaurara matakai wajen tsaron sansanonin, ta samar da abinci da kayan masarufi, da kuma hanyoyin koyar da sana’o’in dogaro da kai ga ’yan gudun hijira — musamman mata da matasa.
Sun kuma bukaci a hukunta duk wanda aka kama da laifin lalata da yara a sansanonin, tare da samar da ingantattun cibiyoyin kula da lafiya domin dakile zubar da ciki ba bisa ƙa’ida ba.
A cewar wani mahalarcin taron, “Wannan matsala ba wai ta Borno ce kawai ba, tana iya bazuwa zuwa sauran jihohi idan ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba.”
Taron ya ƙare da amincewa da kafa kwamitin bin diddigi domin tabbatar da cewa an aiwatar da shawarwarin da aka cimma.