A daren ranar 19 ga wannan wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Amurka Donald Trump sun tattauna ta wayar tarho, inda shugaba Xi ya jaddada cewa, alakar Sin da Amurka na da matukar muhimmanci, Sin da Amurka na iya cimma nasarar bai daya da wadata tare, ta yadda za su amfani kawunansu, da ma sauran sassan duniya baki daya.

A nasa bangare kuwa, shugaba Trump cewa ya yi, alakar Amurka da Sin ita ce mafi muhimmancin dangantaka a duniya, yana mai cewa, aiki tare tsakanin kasashen biyu ka iya haifar da manyan abubuwa da za su ingiza zaman lafiya da daidaito a duniya. Ya yi fatan wanzar da babbar dangantaka mai armashi ta dogon lokaci tsakanin kasarsa da Sin.

A cikin wannan tattaunawar, shugaba Xi ya bayyana ra’ayi da matsayin Sin kan batutuwan dake shafar dangantakar kasashen biyu, ya yi nuni da cewa, ya kamata Sin da Amurka su yi kokari da hadin gwiwa, kana kasar Amurka ta magance daukar matakan kayyade ciniki daga bangare daya, ta haka za a magance kawo illa ga nasarorin da kasashen biyu suka samu yayin shawarwarinsu a zagaye da dama. Game da batun TikTok, ana son ganin kamfanoni su tattauna bisa tushen ka’idojin kasuwanci, da cimma daidaito bisa dokokin kasar Sin da ka’idojin daidaiton samun moriya, ana fatan Amurka za ta samar da yanayin ciniki mai bude kofa da adalci da rashin nuna bambanci ga kamfanonin Sin da suka zuba jari a Amurka. Shugaba Trump ya bayyana cewa, Amurka tana fatan za a ingiza hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin kasashen biyu, kuma zai nuna goyon baya ga tawagogin kasashen biyu da su yi shawarwari don daidaita batun TikTok yadda ya kamata.

Akwai sharhin da aka yi game da cewa, tattaunawar dake tsakanin shugabannin kasashen biyu ta shaida cewa, Sin da Amurka sun samu muhimmin ci gaba kan cimma yarjejeniyar daidaita batun TikTok. Direktan ofishin nazarin siyasar kasa da kasa na kungiyar masana masu nazarin manufofin duniya na kwalejin ilmin zamantakewar al’ummar kasar Sin Zhao Hai ya yi fatan cewa, idan Sin da Amurka suka iya daidaita batun TikTok, to za a samar da sharadi ga kamfanonin kasashen biyu a kan yadda za su yi harkokin kasuwanci a kasuwar kasashen biyu, inda ta hakan za a sa kaimi ga Sin da Amurka wajen ganin sun daidaita sauran batutuwan tattalin arziki da cinikayya baki daya. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

A sa’i daya kuma, kamfanonin kasashen ketare sun samu tabbacin bunkasar kasar Sin ta hanyar halartar bikin na CIIE. Wasu shugabannin kamfanonin kasashen ketare sun bayyana cewa, kasar Sin na da manyan kasuwanni masu bude kofa, da yanayin zuba jari mai dacewa, tare da manufofi masu karko, wadanda suke janyo hankulansu matuka.

 

Haka zalika kuma, a matsayin dandalin shigowa da kayayyaki na musamman a duniya, bikin CIIE ya samar da tabbacin cimma moriyar juna ga kasashen duniya. A bana, a karon farko, an kafa dandalolin nune-nunen kayayyaki daga kasashe mafiya fama da talauci, tare da fadada yankunan nune-nunen kayayyakin kasashen Afirka. A halin yanzu, akwai kamfanoni har 163 daga kasashe mafiya fama da talauci da suka halarci baje kolin na CIIE, adadin da ya karu da kaso 23.5 bisa dari, idan aka kwatanta da na bara. Kana, yawan kamfanoni daga kasashen Afirka ya karu da kaso 80 bisa dari a wannan karo. (Mai Fassara: Maryam Yang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji November 6, 2025 Daga Birnin Sin Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan November 6, 2025 Daga Birnin Sin A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu November 6, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
  • An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
  • Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru
  • Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya
  • Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani
  • Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
  • Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa