Aminiya:
2025-09-24@08:35:39 GMT

Kotun Indiya ta daure dan Najeriya shekara 10 kan safarar miyagun kwayoyi

Published: 24th, September 2025 GMT

Wata kotu ta musamman a Coimbatore da ke kasar Indiya, ta yanke wa wani dan Najeriya mai suna Samson Chukwunonso hukuncin daurin shekaru 10 a gidan yari kan laifin safarar miyagun kwayoyi.

Jaridar Times of India ta ruwaito cewa lamarin ya faro tun a watan Yuli na shekarar 2012, lokacin da jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta India (NCB), reshen Chennai, suka kama wasu fakiti guda uku a ofishin aika sakonni.

An kama ɗan sandan bogi a Kano Sanata Natasha ta koma Majalisar Dattawa

A cikin fakitin, an gano tabar wiwi mai nauyin kilo 1.195 da methaqualone giram 200, wanda darajarsa ta haura kimanin Dalar Amurka 240,000 a kasuwar duniya.

Bincike ya gano cewa fakitin na da alaka da Samson mai shekaru 40, wanda ake zargin yana zaune ba bisa ka’ida ba a kasar.

Jami’an na NCB sun kai samame gidansa inda suka gano ganja kilo 4, lamarin da ya kai ga cafke shi a watan Satumba 2012.

Bayan tambayarsa, an gano cewa Samson yana shirya aika miyagun kwayoyi zuwa kasashen waje ta hanyar kamfanonin aika sakonni, kuma yana da hannu a kungiyoyin safarar kwayoyi na duniya.

A ranar Asabar, 20 ga Satumba, an gurfanar da shi a gaban mai shari’a Rajalingam a kotun musamman da ke karkashin dokar hana safarar miyagun kwayoyi.

An same shi da laifin shirya aika kwayoyi zuwa kasashen waje a matsayin wani bangare na wata babbar kungiyar safarar kwayoyi ta duniya, kuma aka yanke masa hukuncin daurin shekaru 10 a gidan yari tare da tara ₹1 lakh.

Wannan hukunci na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da kama ’yan Najeriya da dama a kasashen Asiya kan laifukan da suka shafi safarar kwayoyi da aikata laifuka na kasa da kasa.

Ko a watan Agusta, sai da ’yan sanda a birnin Kozhikode na kasar ta Indiya suka kama ’yan Najeriya takwas kan zargin safarar kwayoyi.

Jaridar The Hindu ta ce ana zargin su da taka rawa a wata babbar kungiyar safarar kwayoyi da ke da rassa a fadin India.

A wani rahoto makamancin haka, wata kotu ta musamman a gundumar Bengaluru ta yanke wa wani dan Najeriya mai suna Kingsley Samuel hukuncin daurin shekaru 14 kan safarar kwayoyi, lamarin da ke kara nuna yadda ’yan Najeriya ke kara shiga harkar safarar kwayoyi a India.

Yawan kamawa da yanke hukunci ga ’yan Najeriya a kasashen waje na ci gaba da haifar da tambayoyi kan yadda ake kallon Najeriya a idon duniya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Indiya Safarar kwayoyi safarar kwayoyi miyagun kwayoyi yan Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Shettima ya bar Abuja don halartar taron majalisar ɗinkin duniya a New York

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bar Abuja zuwa birnin New York na Ƙasar Amurka, domin halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80.

Taron zai gudana daga ranar Litinin, 22 ga watan Satumba, zuwa ranar Lahadi, 28 ga watan Satumba, 2025.

Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasɗinu Jami’ar European-American ta musanta bai wa Rarara digirin girmamawa

Shettima zai wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wannan babban taro.

Zai gabatar da jawabi, tare da shiga muhawarar shugabannin ƙasashe a zauren taron.

A yayin taron, Mataimakin Shugaban zai kuma bayyana sabbin muradun Najeriya a ƙarƙashin yarjejeniyar kare muhalli.

Wannan zai gudana ne a wani taro na musamman kan sauyin yanayi da Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya zai shirya a ranar Laraba, 24 ga watan Satumba.

Haka kuma, Shettima zai halarci wani taron koli kan samar da gidaje masu sauƙi da sauƙin farashi, wanda Shugaban Ƙasar Kenya zai jagoranta.

Bayan kammala taron, Shettima zai wuce Birnin Frankfurt, na Ƙasar Jamus, inda zai gana da jami’an bankin Deutsche Bank kafin dawowa Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yanke Wa Sojojin Da Suka Sayar Wa ‘Yan Ta’adda Makamai Hukuncin Ɗaurin Rai-da-rai A Borno
  • An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
  • Jihar Kogi Na Cikin Fargaba Yayin Da Kogin Neja Da Benuwe Suka Tumfatsa
  • Burkina Faso, Mali da Nijar sun fice daga Kotun ICC
  • ’Yan sanda sun kama mutum 4 kan kai wa Lakurawa babura a Kebbi
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda
  • Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano
  • Shettima ya tafi New York don halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya
  • Shettima ya bar Abuja don halartar taron majalisar ɗinkin duniya a New York