Aminiya:
2025-11-08@10:06:48 GMT

Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina

Published: 22nd, September 2025 GMT

Ƙaramar Hukumar Sabuwa da ta Ɗandume a Jihar Katsina sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, a wani yunƙuri na kawo ƙarshen hare-hare, kashe-kashe da sace-sacen da suka daɗe suna addabar yankin.

An gudanar da taron sulhun ne a ranar Asabar a ƙauyen Kabalawa Dungun Mua’zu, da ke iyaka da ƙananan hukumomin biyu, amma yana ƙarƙashin Sabuwa.

Da wannan ci-gaban, adadin ƙananan hukumomi da suka ƙulla yarjejeniyar sulhu da ’yan bindiga a jihar ya kai tara.

Sauran sun haɗa da Batsari da Kankara, Kurfi da Musawa da Ɗanmusa da Jibia da kuma Faskari.

Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyu NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu

Shugaban Ƙaramar Hukumar Sabuwa, Sagir Tanimi, da takwaroransa na Ɗandume, Bashir Gyazama, sun halarci taron, inda aka ce su ne suka taimaka wajen cimma yarjejeniyar.

Taron wanda ya ɗauki sa’o’i da dama ya haifar da wasu muhimman matsaya da ɓangarorin biyu suka cimma.

An amince da dakatar da kai hari, inda ’yan bindiga suka yi alƙawarin daina kai hare-hare a ƙauyuka.

Haka kuma an ba su damar shiga garuruwa da ƙauyuka domin harkokin kasuwanci ba tare da tsoron cutarwa daga jama’a ba.

Bugu da ƙari, ’yan bindigar sun yi alƙawarin sako mutanen da suka yi garkuwa da su, sai dai sun roƙi gwamnati ta yi ƙoƙarin ganin an saki ’ya’yansu da ke tsare.

Ɓangarorin biyu sun kuma sha alwashin yin aiki tare domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

A yayin taron, ’yan bindiga da dama sun halarta ɗauke da manyan makamai, tare da shugabanninsu da suka haɗa da Idi Muwage da Alhaji Kabiru da Kachalla Rusku da Kachalla Murtala da Kachalla Mai Saje da Kachalla Dawa da Ardo Abdulsalam Fatika da kuma Alhaji Labi.

Shugaban kwamitin zaman lafiya, Dakta Salisu Ladan, ya bayyana cewa manufar yarjejeniyar ita ce dawo da zaman lafiya mai ɗorewa da kawo ƙarshen kashe-kashe da garkuwa da mutane da sauran munanan ayyuka.

Ya ƙara da cewa, “Shugabannin yankin sun tabbatar wa ’yan bindigar da tsaron rayukansu tare da maraba da su don su ci gaba da gudanar da harkokin kasuwanci a kasuwannin yankin.”

Haka kuma an cimma matsaya cewa za a buɗe kasuwar shanu ta Ɗandume da aka rufe saboda matsalar tsaro, domin bai wa ’yan bindigar damar kawo dabbobinsu da yin ciniki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Ɗandume Sabuwa Zaman lafiya zaman lafiya yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Abba ya yaba wa sojoji kan hallaka ’yan bindiga 19 a Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yaba wa rundunar sojin Najeriya da sauran jami’an tsaro bisa daƙile hare-haren ’yan bindiga a wasu sassan jihar.

Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar.

Kocin Super Eagle ya lashi takobin lashe kofin nahiyar Afirka Mamdani ya zama Musulmi na farko da ya zama magajin garin New York na Amurka

Abba ya yi wannan yabo ne, yayin da yake karɓar babban kwamandan rundunar soji ta 1, a Hedikwatar Kaduna, Manjo Janar Abubakar Sadiq Muhammad Wase, a fadar gwamnati da ke Kano.

Manjo Janar Wase, ya ziyarci Kano domin duba halin tsaro a ƙananan hukumomin Shanono da Tsanyawa.

Ya bayyana yadda mahaifinsa, marigayi Kanal Muhammad Abdullahi Wase, ya taɓa zama kwamishinan soja na Jihar Kano a shekarar 1994.

“Tun lokacin da na karɓi jagorancin rundunar, na ziyarci wuraren da aka kai hare-hare domin na yaba wa jarumtar sojojimmu,” in ji Janar Wase.

Gwamnan ya gode wa sojoji bisa jajircewarsu, tare da jinjina wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan naɗa sabbin hafsoshin tsaro masu ƙwazo da kishin ƙasa.

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar za ta bayar da kyautar motoci ƙirar Hilux guda 10 da babura 60 ga rundunar haɗin gwiwa da ke aiki a yankunan da abin ya shafa.

Haka kuma ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro wajen yaƙi da ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da kuma satar shanu.

Idan ba a manta Aminiya ta ruwaito yadda dakarun soji suka daƙile hari tare da kashe ’yan bindiga 19 a yankin Shanono yayin wani samame da suka kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Tinubu ya gana da Sarkin Musulmi a Aso Rock
  • Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
  • Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Qalibaf: Iran Da Pakistan Zasu Aiwatar Dukkan Yarjejeniyar Da Suka Cimma A Tsakaninsu
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
  • An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita
  • Abba ya yaba wa sojoji kan hallaka ’yan bindiga 19 a Kano