Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasɗinu
Published: 21st, September 2025 GMT
Ƙasar Birtaniya a wannan Lahadin za ta amince a hukumance da kafa ƙasar Falasɗinu a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta.
Birtaniya wadda ta daɗe tana goyon bayan Isra’ila za ta juya mata baya, sakamakon hare-haren da Isra’ilar take kai wa Zirin Gaza, wanda ya samo asali bayan da ƙungiyar Hamas ta kai wani mummunan hari a ranar 7 ga watan Oktoban 2023.
Tun a watan Yulin wannan shekarar Firaministan Birtaniya, Keir Starmer ya ce zai goyi kafa ƙasar Falasɗinu yana mai gindaya wa Isra’ilar sharaɗin yanke wannan shawarar.
Starmer ya ce zai amince da ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ilar ba ta ɗauki wani ƙwaƙƙwaran mataki na cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da Hamas ba kafin babban taron Majalisar Dinkin Duniya na watan Satumba.
Kafafen yada labarai sun ruwaito cewa, Starmer zai yi jawabi ga al’umma kan matsayarsa, gabanin babban taron zauren majalisar Dinkin Duniya, inda ƙasashe 10 ciki har da Faransa za su amince da kafa ƙasar ta Falasɗinu.
Sai dai Amurka da Isra’ila sun soki matakin, suna bayyana shi a matsayin saka wa Hamas duk da harin da ta kai na ranar 7 ga watan Oktoban 2023.
Su ma ƙasashen Portugal da Canada da Australia sun ce za su amince da ƙasar Falasɗinun a cikin wannan mako.
Daga gobe Litinin ce sama da shugabannin ƙasashe 140 ne za su hallara a birnin New York domin taron shekara-shekara na Majalisar Ɗinkin Duniya.
Matsalar jinƙai da ta addabi yankin Falasɗinu za ta kasance a kan gaba a tattaunawar da za ta gudana a taron na bana.
Shugaba guda da ba zai halarci taron a zahiri ba shi ne shugaban Falasɗinawa, Mahmud Abbas, wanda Amurka ta hana biza tare da waɗansu jami’ansa.
A karo na musamman, babban zauren ya kaɗa ƙuri’a a ranar Juma’a domin bai wa Abbas damar gabatar da jawabi ta hanyar bidiyo, yayin da jakadan Falasɗinu zai wakilce shi a cikin ɗakin taron.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Birtaniya Isra ila ƙasar Falasɗinu
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba
Majalisar Tsaro ta Sudan ta ƙi amincewa da duk wani shirin tsagaita wuta, tana mai gindaya sharadin cewa sai dai idan (RSF) ta janye daga biranen da ta kwace iko da su.
Majalisar ta bayyana wannan matsayin ne a wani taro da aka gudanar a babban birnin Khartoum, don mayar da martani ga shawarar tsagaita wuta da Amurka ta gabatar.
A cewar majiyoyin, majalisar ta yanke shawarar ci gaba da kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana da kuma yin gangami don tunkarar abin da ta bayyana a matsayin “tawaye da makirci.” Majalisar ta kuma yi kira da a kafa sojojin sa kai na al’ummar kasa don tallafawa sojoji wajen tunkarar RSF.
Wata majiya ta shaida wa Al-Mayadeen cewa Sojojin Sudan suna yin gagarumin shirin yaki a bangarorin Kordofan da Darfur. Rahotanni sun ce sojoji sun yi watsi da tsagaita wuta har sai an sake kwace muhimman wurare daga hannun RSF.
Wani bayanin da ba a tabbatar da shi a hukumance ya yi nuni da cewa, Majalisar Tsaro ta Sudan, wacce shugaban Majalisar Mulkin Soja kuma shugaban rundunar sojojin Abdel Fattah al-Burhan ke jagoranta, za ta tattauna batun shirin tsagaita wuta da Amurka ta gabatar da nufin kawo karshen rikicin Sudan, a cewar wata majiya da ta tabbatar da hakan ga kamfanin dillancin labaran AFP.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Masu Sa Ido na Tarayyar Afirka: Zaben Tanzania Ya Keta Ka’idojin Demokradiyya November 6, 2025 An Kama ‘Yan Jarida 3 A Nijar Bisa Tuhumar Fitar Da Bayanai Na Hukuma November 5, 2025 Sudan Ta Sake Jaddada Tuhumar Kasar UAE Da Taimakon Rundunar RSF November 5, 2025 Shugaban Mali Ya Yi jawabi Akan Hana Shigar Da Man Futur Da Masu Ikirarin Jihadi Suke Yi November 5, 2025 Iran : bisa sharadi ne muka saki ‘yan Faransa daga gidan yari November 5, 2025 Gaza : MDD Ta damu kan keta yarjejeniya tsagaita wuta da Isra’ila ke yi November 5, 2025 Kungiyoyin agaji sun ce tallafin da ake bai wa Gaza bai isa ba November 5, 2025 China ta yi alkawarin ci gaba da tallafawa Najeriya bayan barazanar Trump November 5, 2025 Imam Khamenei: Rikici Tsakanin Iran da Amurka na asasi ne November 5, 2025 Iravani: Kalaman Trump barazana ne ga zaman lafiyar duniya November 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci