’Yan bindiga sun kai hari sakatariyar ’yan jarida ta jihar Yobe
Published: 19th, September 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga da ba a san ko su waye ba sun kai hari a sakatariyar Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) da ke Damaturu, babban birnin jihar Yobe, da sanyin safiyar Juma’a.
Rahotanni sun ce yayin harin, maharan sun harbi wani jami’in ɗan sanda da ke gadin sakatariyar suka ji masa rauni ƙafa.
An dakatar da shugabannin sakandare 6 a Sakkwato kan zargin cin amanar aiki Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan buƙatar MDD ta tsagaita wuta a GazaLamarin dai ya faru ne da misalin ƙarfe 2:00 na dare, inda maharan suka buɗe wuta.
Shugaban ƙungiyar NUJ reshen jihar, Rajab Ismail Mohammed, ya bayyana harin a matsayin abin tayar da hankali da kuma babbar barazana ga lafiyar ’yan jarida a jihar.
Ya yi kira ga jami’an tsaro da su gaggauta gudanar da bincike kan lamarin tare da gurfanar da maharan a gaban kotu.
Ƙungiyar ta kuma yi kira ga hukumomi da su ƙara ƙaimi wajen samar da tsaro ga ƙwararrun kafafen yaɗa labarai da cibiyoyin yaɗa labarai a faɗin jihar, inda ta jaddada cewa irin waɗannan hare-hare na iya kawo cikas ga ’yancin ’yan jarida da kuma samun damar yin amfani da bayanan jama’a.
Ƙungiyar ta jaddada cewa kare ‘yan jarida na da matuƙar muhimmanci ga ci gaban dimokuraɗiyya da riƙon amanar jama’a.
Yanzu haka dai dan sandan da aka harba na can a sashin gaggawa na asibitin ’yan sanda da ke Damaturu.
Rahotanni sun ce hukumomin ’yan sanda sun fara gudanar da bincike domin gano waɗanda ke da hannu a lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Yaba Da Tasirin Shirin NG-CARES A Jihar Jigawa
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na fadada ayyukan ci gaban karkara, tare da aiwatar da shirye-shiryen da za su inganta rayuwar al’umma.
Gwamnan ya bayyana haka ne lokacin da ya karɓi bakuncin jami’in kula da shirin rage radadin illar da annobar cutar Korona ta haifar, wato (NG-CARES), Dakta Abdulkareem Obaje, wanda ya kai masa ziyara ta ban girma a Dutse.
Dakta Obaje ya yaba wa gwamnan da gwamnatin jihar Jigawa bisa goyon bayan da suke bai wa shirin NG-CARES tun daga lokacin da aka ƙaddamar da shi a shekarar 2021.
Ya bayyana cewa an kirkiro shirin ne a shekarar 2020 sakamakon tasirin annobar COVID-19, domin taimaka wa jihohi su farfaɗo da tattalin arziƙin karkara da tallafa wa marasa ƙarfi.
“Shirin NG-CARES ya kai shekaru huɗu yana gudana, kuma mun biya jihohi kuɗaɗe har zuwa dala miliyan 696, inda aka taimaka wa mutane kusan miliyan 70 a fadin ƙasar nan.” In ji Dakta Obaje.
Ya ƙara da cewa shirin, wanda ya fara da jimillar dala miliyan 750, ya ba da dama ga jihohi irin su Jigawa su taka muhimmiyar rawa wajen aiwatar da ayyuka da suka taɓa rayuwar jama’a kai tsaye.
Dakta Obaje ya kuma bayyana cewa sabon zagaye na shirin, NG-CARES 2.0, zai fara aiki nan ba da jimawa ba.
A nasa jawabin, Gwamna Namadi ya gode wa tawagar NG-CARES bisa ziyarar da suka kai masa, tare da bayyana shirin a matsayin ɗaya daga cikin manyan shirye-shiryen da suka fi tasiri wajen kai tallafi kai tsaye ga al’umma mafi ƙaranci a Jihar Jigawa.
“NG-CARES shi ne shirin da ya fi taɓa rayuwar jama’armu kai tsaye.” In ji shi.
Ya tunatar da yadda ya yi ƙoƙari wajen ganin an ci gaba da aiwatar da shirin a matakin Majalisar Gwamnonin Najeriya (NGF) da kuma Babban Bankin Duniya (World Bank).
“Ina iya cewa ba tare da wata shakka ba, NG-CARES 2.0 ra’ayinmu ne, domin mu ne muka nemi a ci gaba da shirin.” In ji Gwamna Namadi.
Gwamnan ya kuma yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da tallafa wa shirin domin ƙarfafa hanyoyin kyautata rayuwa da kuma inganta tsaron zamantakewa a tsakanin jama’a.
Ziyarar ta kasance wani ɓangare ne na zagayen da ofishin NG-CARES ke yi a fadin ƙasa domin tattara rahotanni, jin ra’ayoyin jama’a, da kuma nuna nasarorin da aka samu yayin da ake shirin kaddamar da NG-CARES 2.0.