A ci gaba da kokarin da take yi na tsaftace harkar ilimi, wata kotu a Kano ta bayar da umarnin rufe wasu makarantu masu zaman kansu nan da nan, 6 saboda saba ka’idojin jihar da suka hada da kara kudin makaranta da kuma tilasta iyayen yara sayan litattafai na dole da sauran tsarabe-tsarabe da suka dorawa iyayen yara.

 

Sakataren zartarwa na hukumar kula da cibiyoyi masu zaman kansu da sa kai na jihar Kano (KSPVIB), Kwamared Baba Abubakar Umar ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai.

 

A cewarsa, makarantun da abin ya shafa sun hada da Prime College, Darul Ulum, Gwani Dan Zarga College, Unity Academy, Dano Memorial Academy, da Auwa Academy.

 

Ya yi nuni da cewa hukumar tana kuma jiran umarnin kotu na rufe makarantar Nurul Islam da kwalejin As-Saif.

 

“Makarantun sun kara kudade ba tare da bin ka’idojin da suka dace ba, kuma sun kasa mika jerin sunayen litattafai yadda ya kamata ga iyaye, da sauran laifuka,” in ji Baba Umar.

 

Sakataren zartarwa wanda ya zama mai ba gwamna shawara na musamman kan cibiyoyi masu zaman kansu da na sa kai ya bayyana cewa an umurci makarantun da abin ya shafa da su dakatar da duk wasu harkokin ilimi har sai an kammala zaman kotun da aka shirya yi a ranar 30 ga Satumba da 7 ga Oktoba, 2025.

 

Baba Umar ya ci gaba da cewa gwamnatin jihar ta kafa ofisoshin shiyya ta KSPVIB a fadin kananan hukumomi 44 domin sa ido da kuma dakile haramtattun makarantu da kuma cibiyoyin da ke bijirewa dokokin jihar.

 

Ya jaddada cewa gwamnati a karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta baiwa ilimi fifiko, inda ya nuna cewa a cikin sama da makarantu masu zaman kansu da na sa kai sama da 7,000 da ke Kano, kusan 2,700 ne kawai ke da rijista.

 

“Tarin bayanai yana da mahimmanci don ingantaccen tsarin ilimi, tsara tsarin karatu, tura malamai masu inganci, da samar da ingantaccen yanayin koyo,” in ji shi.

 

Yayin da yake bayyana mahimmancin makarantu a cikin tsarin ilimi, ya jaddada cewa masu mallakar su dole ne su bi ka’idoji.

 

“Ba ma son rufe ko dakatar da makarantu, amma da yawa daga cikin masu hannun jari suna ganin sun fi karfin bin doka, ina so in tabbatar muku da cewa a jihar Kano, babu wata makaranta da ta fi karfin doka,” in ji shi.

 

Ya kuma yi kira ga iyaye da su tabbatar da biyan kudaden makaranta a kan lokaci, domin hakan yana baiwa makarantu damar biyan albashin ma’aikata da inganta tsarin ilimi.

 

Kwamared Umar ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ganin ta bunkasa ilimi a duniya.

 

COV/Khadija Aliyu

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Makarantu Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Kazalika, masu sukar na ganin cewa, gwamnatin ta yi watsi da irin halin ƙuncin rayuwa da musamman
talakwan ƙasar, ke ci gaba da fuskanta, kamar dai, na ci gaba da hauhawan farashin kayan masarufi da
ƙarin kuɗin Man Fetur da ƙarin kuɗin wutar lantarki da ƙarancin albashin da ake biyan ma’aikata,
musamman na gwamnati, wanda a baya, ta yi alƙawarin lalubo masu da mafita.

Wannan batun na ƙarin albashin, tamkar dai wani cin zarafi wanda kuma abu ne, da ke tattare da hatsari.
Kusan tun lokacin da shugaba Bola Tinubu, ya ɗare Karagar shugabancin ƙasar, ya rage yawan kuɗaɗen
da ake kashewa, na gudanar da mulki, inda gwamtainsa, ta rage yawan ɗimbin tawagar da take kwasa, na
yin tafiye-tafiye, musamman zuwa ƙasashen duniya.
Amma batun na ƙarawa ƴ an siyasa masu riƙe da madafun ikon, a wannan yanayin da ƙasar ke a ciki,
tamkar mayar da Agogo baya ne.
Misali, gwamnatin har zuwa yau, ta gaza wajen cika ɗaukacin buƙatun ƙungiyoyin manyan makaratun
ƙasar wato ASU da kuma ASUP, inda kuma a gefe ɗaya, ƙungiyoyin ƙwarrun likitoci, suma suke ta kai
gwauro da mari, na neman gwamnatin, ta biya masu na su buƙatun
Saboda rashin biya masu buƙatun na su, suke tsunduma cikin yajin aiki na gargaɗi ko kuma gargaɗi.

Hakazalik, a yayin da ƙasar ke jigelon kashe kuɗaɗe, na gudanar da wasu ayyuka a ƙetare, amma a gife
ɗaya, an bar ma’aikata na karɓar mafi ƙarancin alabshin na Naira 70,000 kacal, inda wannan kuɗin, ba zai
iya kawar masu koda da ƙishirwarsu ba, duba da hauhawan kayan masarufi, da ake ci gaba da fuskanta a
ƙasar.

Akasarin ma’aikata a ƙasar, na ci gaba da kasance wa ne a cikin talauci, inda kuma sauran ƴ an siyasa, ke
ci gaba da yin wadaƙa.
Maimakon ƙarin albashin kamata yi Hukumar ta fara tunanin fara yiwa albashin ma’aikatan gwamnati
garanbawul da kuma inganta rayuwarsu.A yayin da ƙasar ke ci gaba da fuskantar ƙaranci kuɗi tare da kuma yadda alummar ƙasarke ci gaba da
fitar da rai ga alƙawarin da gwamnatin shugaba Tinubu ta yi, na saita ƙasar, batun na yin ƙarin, a wannan
lokacin, wani abin dubawa ne.
Wannna Jaridar ta nuna takaicinta kan wannan batun, musamman duba da cewa, yunƙurin na Hukumar,
na ci gaba da fuskantar suka.

Bugu da ƙari, duba da cewa, Nijeriya kusan ta dogara ne kachokam, kan ciwao bashi daga ƙetare, domin
ci giɓin da take da shi, a cikin kasafin kuɗinta, wanda hakan ya saɓawa ƙa’ida, a saboda haka, batun na
ƙarin albashin ga ƴ an siyasa, tamkar zuba kuɗi ne, a inda bai kamata ba.
Ya zama wajibi, gwamnatin ta dakatar da wannan batun na ƙarin albashin ga ƴ an siyasa masu riƙe da
madafun iko, amma ta mayar da hankali, wajen gudanar da bin diddigin kashe kuɗaɗe wanda zai yi daidai
da, tsarin tattalin arzikin ƙasar, a zahirance da kuma gudanar da ƙa’idojin gudanar da aikin gwamnati.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Sauya Sunan Ma’aikatar Mata
  • Jigawa Na Gabatar Taro A Abuja Domin Tattara Bayanin Kasafin Kudin 2026
  • Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
  • Mutum 1,666 ne suka kashe kansu a Legas cikin shekaru biyar – ’Yan sanda
  • Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
  • ’Yan sanda sun kama mutum 9 kan yin garkuwa da kansu
  • Uwargidan Shugaban Kasa, Oluremi Tinubu Ta Yi Kira Ga Zaman Lafiya A Duniya
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna