Al’ummar Jihar Sakkwato na cike da fargaba da alhini bayan da wasu mazauna kauyuka da dama suka rasu a hatsarin kwale-kwale a Karamar Hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato.

Lamarin ya faru ne lokacin da jama’a ke tserewa daga wani sabon harin da ‘yan ta’addan Lakurawa suka kai, inda kwale-kwalen da ke dauke da mutane fiye da kima ya kife.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na Rundunar ‘Yan sandan Jihar Sakkwato, ASP Abubakar Rufa’i, ya tabbatar da aukuwar lamarin ga wakilin Rediyon Najeriya a jihar.

ASP Abubakar ya ce har yanzu ba a tantance adadin mutanen da suka shiga kwale-kwalen ba, yana mai jaddada cewa ana ci bincike da aikin ceto.

Wani shaidan gani da ido, wanda bai so a bayyana sunansa ba ya shaida wa Rediyon Najeriya cewa wadanda lamarin ya rutsa da su mutanen kauye ne da suka tsere daga matsin lambar ‘yan bindigar Lakurawa.

Wannan hatsarin shi ne na huɗu da ya yi sanadiyyar rasa rayuka a cikin watanni biyu a Sakkwato, lamarin da ya haifar da fargaba kan matsalar tsaro da kuma hatsarin shiga kwale-kwale a yankin.

Mazauna Sabon Birni da kauyuka makwabta na ci gaba da zama cikin zullumi, inda miyagu ke kafa shingayen bincike, kona gonaki da korar jama’a daga kauyuka.

Rediyon Najeriya ta ruwaito cewa iyalan da suka rasa ‘yan uwansu sun yi cirko-cirko a bakin kogin, yayin da masu aikin ceto ke ci gaba da nemo wadanda suka bace.

 

Daga Nasir Malali

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hatsarin Kwale kwale Lakurawa Sakkwato kwale kwale

এছাড়াও পড়ুন:

Gidan rediyo ya ɗauki nauyin sanya yara 40 a makaranta a Kano

Himma Radio, wani gidan rediyon al’umma da ke Jihar Kano, ya sanya yara 40 a makarantar firamare a ƙaramar hukumar Madobi.

An gudanar da bikin kaddamar da shirin ne a ranar Lahadi a harabar gidan rediyon da ke Madobi, da nufin rage yawan yara da ke gararamba a titunan jihar ba tare da zuwa makaranta ba.

An kashe ’yan bindiga 19 yayin wani hari a Kano Komai zai iya faruwa a hare-haren da za mu kai Nijeriya — Trump

Shugaban gidan rediyon, Ismail Yusuf Makwarari, ya ce wannan shiri wani ɓangare ne na aikin al’umma da gidan rediyon ke yi, kuma suna da burin faɗaɗa shi zuwa dukkanin ƙananan hukumomin jihar 44.

Ya ce, “Mu gidan rediyon al’umma ne da ke mayar da hankali kan harkar noma, kuma mun himmatu wajen inganta ci gaban yankunan karkara.

“Mun ƙaddamar da wannan shiri mai taken ‘Gangamin dawo da yara makaranta’ a matsayin wata hanya ta nuna cewa ilimi da noma su ne ginshiƙan ci gaba mai ɗorewa.”

Ya ƙara da cewa, “Mun zo da wannan tunani ne domin taimaka wa al’ummar da ke sauraron shirye-shiryenmu saboda Allah.

“A matsayina na shugaban kafar yaɗa labarai, mun ga cewa ba wai kawai mu riƙa fallasa matsalolin da ke cikin harkar ilimi ba ne, amma mu ma za mu iya taka rawa wajen kawo sauyi.”

Daga nan sai ya buƙaci sauran ƙungiyoyi da kamfanoni da su yi koyi da irin wannan aiki a matsayin gudummawarsu ga ci gaban ƙasa.

Hakimin Madobi kuma Majidadin Kano, Musa Saleh Kwankwaso, ya gode wa gidan rediyon bisa wannan hoɓɓasan da ya yi, tare da roƙon sauran masu hannu da shuni da su yi koyi da shi.

“Ilimi haƙƙin kowa ne, gwamnati ba za ta iya ɗaukar nauyin komai ita kaɗai ba. Irin waɗannan ƙungiyoyi da mutane su ma su shigo su taimaka. Muna farin ciki da wannan mataki da Himma Radio ta ɗauka,” in ji Hakimin.

Shugaban Jami’ar Bayero Kano (BUK), Farfesa Haruna Musa, wanda shi ma ya halarci bikin, ya ce Najeriya da ke da yawan jama’a sama da miliyan 200, waɗanda kuma fiye da rabinsu matasa ne, akwai buƙatar haɗa kai wajen tallafa wa fannin ilimi.

Ya kuma tabbatar da cewa ƙofar jami’arsa a buɗe take don haɗin gwiwa da duk masu ruwa da tsaki don ganin ta bunƙasa ilimi musamman a yankunan karkara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara
  • KADUNA TA ZAMA JIHAR FARKO A NIJERIYA DA TA AIWATAR DA SHIRIN SAMAR DA ABINCIN MAI GINA JIKI GA YARA – UNICEF
  • An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan Bayelsa
  • Gidan rediyo ya ɗauki nauyin sanya yara 40 a makaranta a Kano
  • ’Yan Sandan Legas sun ayyana neman Sowore ruwa a jallo
  • Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT
  • Sudan : Mutane 1,500 sun rasa matsugunansu sakamakon tashin hankali
  • Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano