Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote
Published: 20th, September 2025 GMT
A baya, ƙasashe biyu kawai na Afirka ba sa shigo da man fetur, amma abin takaici, yanzu sun koma shigo da kaya. Wannan yana da illa ga Afirka,” in ji shi.
Dangote ya bayyana cewa aikin masana’antar ya kasance mai haɗari sosai. Ya ce ya samu gargaɗi sau da dama daga masana harkokin mai, masu zuba jari, da jami’an gwamnati na cikin gida da waje, waɗanda suka yi jayayya cewa irin wannan aikin masana’antar mai girma manyan ƙasashe ne kaɗai ke iya yi, ya amince cewa da aikin ya gaza, zai rasa dukiyoyinsa ga masu ba da rance.
“Yanke shawarar gina masana’antar ba abu ne mai sauƙi ba. Idan ya gaza, masu ba da rance za su daka wawa a dukiyoyinmu. Amma mun yi imani da Nijeriya da Afirka,” in ji shi.
Duk da adawar da ƙalubalen tattalin arziki, masana’antar ta rage farashin man fetur daga kusan Naira 1,100 kafin fara samarwa zuwa Naira 841 a yankunan Kudu maso Yamma, Abuja, Delta, Riɓers, Edo, da Kwara. Tare da ci gaba da amfani da motoci masu amfani da CNG, Dangote na sa ran wannan rage farashin da zai shafi ƙasa baki ɗaya nan ba da jimawa ba.
Dangote ya jaddada cewa manufar masana’antar ba ta maye gurbin ma’aikata ba, sai dai tana ƙirƙirar dubban sabbin damar aiki. Ana sa ran amfani da motoci 4,000 masu amfani da CNG zai samar da aƙalla ayyuka 24,000 a faɗin Nijeriya.
“Ba mu maye gurbin ma’aikata ba; muna ƙirƙirar ayyuka da yawa. Motocin CNG ba za su yi aiki da robot ba. Ma’aikatanmu na karɓar albashi sau uku fiye da mafi ƙarancin albashi. Direbobinmu na samun albashi mai rai, inshorar rayuwa, inshorar lafiya da ke rufe su, matan su, da har zuwa yara huɗu, har da fansho na rayuwa. Ba wai kawai muna ɗaukar direbobi ba, har ma da masu gyaran mota, manajoji na jirgin motoci, da sauran ƙwararru don tallafawa jirgin motoci na CNG.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: masana antar
এছাড়াও পড়ুন:
Fitaccen ɗan wasan tseren motoci Jenson Button zai yi ritaya
Shahararren ɗan wasan tseren motoci, Jenson Button, ya bayyana cewa gasar tseren Bahrain na sa’o’i takwas da za a gudanar a ƙarshen mako, ita ce za ta zama ta ƙarshe da zai yi a wasannin ƙwararru na tseren motoci.
Button ɗan asalin kasar Birtaniya, wanda yake da shekaru 45, ya shafe shekaru biyu da suka gabata yana fafatawa a gasar World Endurance Championship (WEC) tare da ƙungiyar Jota.
Tsohon gwarzon Formula 1 ɗin ya taɓa lashe Gasar Duniya ta Formula 1 a shekarar 2009 tare da ƙungiyar Brawn, kafin ya yi ritaya daga F1 a 2016 — bayan fafatawa a wasanni 306 cikin shekaru 18 na aikinsa, inda ya lashe Grand Prix sau 15.