Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-08@10:06:48 GMT

CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya

Published: 22nd, September 2025 GMT

CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya

 

Haddadiyar Kungiyoyin Makiyaya na kasashen Africa (CORET) ta bayyana cewa an samu karin yawan ɗalibai a makarantun makiyaya cikin watanni goma da aka fara shirin ciyar da ɗalibai.

 

Babban Sakataren CORET, Muhammed Bello Tukur, ya bayyana haka a taron kwana ɗaya da aka gudanar a Kaduna domin ƙara wa ma’aikata da abokan hulɗarsu ƙwarewa kan harkar ciyar da ɗalibai.

 

Taron ya mayar da hankali ne wajen duba nasarorin da aka samu cikin watanni goma tun lokacin da aka fara shirin a Ladduga, Karamar Hukumar Kachia ta Jihar Kaduna, da kuma Maigatari a Jihar Jigawa.

 

Babban Sakataren CORET, Muhammed Bello Tukur, ya bayyana cewa shirin ya shafi makarantun makiyaya kawai a jihohin Jigawa da Kaduna.

 

Ya ce ciyarwa na daga cikin manyan matsalolin da ke sa yara barin makarantu, don haka shirin ya ƙunshi amfani da al’ummomin yankuna wajen samar da abincin ɗalibai.

 

Ya ƙara da cewa an sayi kayan abinci daga cikin al’umma tare da haɗa su wajen tabbatar da ingancin abincin da ɗalibai ke ci. Bugu da ƙari, CORET ta samar da rijiyoyin burtsatse domin tabbatar da samun ruwa na sha da na yau da kullum.

 

Muhammed Bello Tukur ya yaba da irin goyon bayan da abokan hulɗa musamman ECOWAS, da kuma Gwamnatin Tarayya da Jihohi ke bayarwa wajen tabbatar da nasarar shirin.

 

A nasa jawabin, Ko’odinatan Shirin, Dakta Abdu Umar Ardo, ya bayyana cewa shirin ya zama nasara daga komai zuwa abu mai amfani tun da jihohin suka rungumi karatun ’ya’yan makiyaya.

 

Haka kuma, a kasidarsa, Bashir Abbo ya bayyana cewa bincike ya nuna akwai bukatar ƙwararrun malamai, farfaɗo da kwamitocin gudanar da makarantu da ƙarfafa ƙungiyoyin mata domin su riƙa taka rawar da ta dace.

 

Ya ce ɗaukar ƙarin malamai ƙwararru zai samar da sakamako mai kyau nan gaba.

 

Mahalarta taron sun fito ne daga Ladduga, yayin da wasu daga cikin mahalarta daga Karamar Hukumar Maigatari ta Jihar Jigawa suka halarci taron ta yanar gizo.

COV: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

 

Wannan matakin ya zo ne a daidai lokacin da Amurka ke ci gaba da nuna damuwa kan abin da ta bayyana a matsayin cin zarafin Kiristoci da sauran tsirarun addinai a Nijeriya.

 

Dan majalisa Smith ya yaba wa shugaban Amurka Donald Trump kan ayyana Nijeriya a matsayin ‘Kasar da ke da damuwa ta musamman’ (CPC), inda ya ambato cewa, akwai rahotanni da ke cewa, ana kai wa Kiristoci hare-hare a sassan jihohin Benuwe da Filato.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama November 6, 2025 Manyan Labarai Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro November 6, 2025 Manyan Labarai Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu  November 5, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
  • Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya
  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
  • Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya
  • Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa
  • An amince da hukuncin yi wa malamai ɗaurin shekara 14 kan lalata da ɗalibai
  • Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Abba ya yaba wa sojoji kan hallaka ’yan bindiga 19 a Kano