Leadership News Hausa:
2025-09-20@23:30:30 GMT

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

Published: 21st, September 2025 GMT

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

A gun liyafar murnar cika shekaru 76, da kafa Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin da ofishin jakadancin Sin dake Birtaniya ya shirya a jiya Jumma’a 19 ga wata, an gabatar da wani fim mai taken Shen Zhou 13, fim din kasar Sin na farko da aka dauka kai-tsaye a sararin samaniya kuma bisa fasahar 8K, wadda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar wato CMG ya tsara.

Wannan ne karo na farko da aka gabatar da fim din a kasashen waje.

Al’ummun kasar Birtaniya daga bangarori daban daban, da jami’an diflomasiyyar kasa da kasa dake Birtaniya, gami da Sinawa dake zaune a kasar sama da 400, sun halarci liyafar.

Wasu ’yan saman jannati uku na kumbon Shenzhou-13, wato Zhai Zhigang, Wang Yaping, da Ye Guangfu, su ne suka dauki wannan fim, wanda ya shaida yadda suke aiki, da rayuwa na tsawon watanni shida a tashar binciken sararin samaniya ta Sin. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

Ta ce tun bayan da Sin da UNESCO suka kafa wannan dandali na gabatar da lambobin yabo a fannin raya ilimin yara mata da mata a shekarar 2015, kawo yanzu, a mika jimillar irin wadannan lambobi 20 ga ayyuka daban daban da suka cancanta daga kasashe 19. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni
  • Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?
  • Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco
  • Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 
  • Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu
  • Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata
  • Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin
  • Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
  • Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar