Leadership News Hausa:
2025-11-05@08:42:17 GMT

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

Published: 21st, September 2025 GMT

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

A gun liyafar murnar cika shekaru 76, da kafa Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin da ofishin jakadancin Sin dake Birtaniya ya shirya a jiya Jumma’a 19 ga wata, an gabatar da wani fim mai taken Shen Zhou 13, fim din kasar Sin na farko da aka dauka kai-tsaye a sararin samaniya kuma bisa fasahar 8K, wadda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar wato CMG ya tsara.

Wannan ne karo na farko da aka gabatar da fim din a kasashen waje.

Al’ummun kasar Birtaniya daga bangarori daban daban, da jami’an diflomasiyyar kasa da kasa dake Birtaniya, gami da Sinawa dake zaune a kasar sama da 400, sun halarci liyafar.

Wasu ’yan saman jannati uku na kumbon Shenzhou-13, wato Zhai Zhigang, Wang Yaping, da Ye Guangfu, su ne suka dauki wannan fim, wanda ya shaida yadda suke aiki, da rayuwa na tsawon watanni shida a tashar binciken sararin samaniya ta Sin. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya? November 2, 2025 Ra'ayi Riga Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani October 28, 2025 Ra'ayi Riga Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka? October 27, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
  • Dalilin da Trump ya yi iƙirarin ana kisan Kiristoci a Nijeriya — Ndume
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Prime Ministan Sudan Yayi Gargadi Game Da Aikewa Da Dakarun Tabbatar Da Zaman Lafiya Kasar
  • Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin
  • Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
  • NAJERIYA A YAU: Ko Kawo Dakarun Kasar Amurka Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya