Aminiya:
2025-09-19@20:31:08 GMT

Sauya Sheƙa: Kwankwaso ya gindaya sharuɗa kafin sake komawa APC

Published: 19th, September 2025 GMT

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce jam’iyyarsa a shirye ta ke, ta haɗa kai da APC, idan an shirye karɓar sharuɗansu.

Kwankwaso, ya faɗi haka ne a gidansa da ke Miller Road a Kano, lokacin da ya karɓi baƙuncin tsohon jigon APC a jihar, Buhari Bakwana, tare da wasu jiga-jigai.

Babu wani hari da aka kai sakatariyar NUJ a Yobe — ’Yan Sanda An cafke mutum 6 kan tono gawa a kabari don yin asiri a Gombe

Ya bayyaa musu yadda shi da wasu ’yan siyasa wajen kafa jam’iyyar APC a 2013 kuma sun sha wahala kafin kafuwarta.

“Babu wanda zai faɗa min irin wahalar da muka sha wajen kafa APC. Mu ne muka jagoranci kafuwar jam’iyyar, mu ne kuma gwamnoni bakwai na farko da muka ba ta goyon baya.

“An yi amfani da ICPC, EFCC, da ’yan sanda a kaina a wancan lokaci don hana mu cimma burinmu,” in ji shi.

Kwankwaso ya ce duk wata tattaunawa ta haɗin gwiwa ko komawa APC dole ta tabbatar da alfanun da NNPP za ta samu.

“Idan kuna so mu koma APC, dole ku faɗa mana abin da NNPP za ta amfana da shi. Muna da ’yan takarar gwamna a duk jihohi da cikakken tsari a faɗin ƙasar nN. Me za ku ba su idan muka shiga?” ya tambaya.

Ya kuma tunatar da yadda APC da PDP suka saɓa yarjeniyoyin da suka yi a baya.

“Shekaru takwas na APC a ƙarƙashin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ba su ba mu komai ba, ko godiya ba su mana ba.

“A PDP, abin da muka nema kawai shi ne shugabancin jam’iyyar a yanki guda, amma suka ƙi ba mu. Mun bar su lafiya, kuma yau mun ƙara ƙarfi da ƙima,” in ji shi.

Jagoran na NNPP, ya ƙara da cewa jam’iyyarsa a shirye ta ke don yin tattaunawa, amma ya yi gargaɗin cewa ba za ta yadda a yi amfani da ita sannan a watsar da ita ba.

“Mun shirya shiga APC bisa sharuɗa da cikakkun alƙawura. Ba za mu yadda wani ya yi amfani da mu a jefar da mu ba,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alƙawari Kwankwaso Sauya Sheƙa Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

A cewarsa, jihar ta ba da fifiko wajen samar da kudade, kayayyakin more rayuwa, da kuma samun damar koyo tun bayan hawansa kujerar mulki.

 

Gwamnan ya kara da cewa, yadda gwamnatinsa ta mayar da hankali kan ilimin ’ya’ya mata, bayar da tallafin karatu, da rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, ya taimaka wajen kawo sabon matsayi a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin
  • 2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP
  • Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025
  • ’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa
  • Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
  • HOTUNA: Yadda dubban magoya baya suka yi dafifi don tarbar Fubara
  • Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu