Hatsarin mota ya yi ajalin mutum 4, 16 sun jikkata a Yobe
Published: 21st, September 2025 GMT
Aƙalla mutum ne sun rasu, yayin da wasu 16 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya auku a Ƙaramar Hukumar Karasuwa, a Jihar Yobe.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Yobe, SP Dungus Abdulkareem ne, ya tabbatar da faruwar hatsarin ya faru a ranar Asabar da misalin ƙarfe 2:50 na rana a ƙauyen Zangon Kanwa.
Hatsarin ya rutsa da mota ƙirar Toyota Hiace wadda ke ɗauke da fasinjoji daga Jakusko zuwa kasuwar Jajimaji da kuma mota ƙirar Volvo daga garin Azare.
Rahoto ya nuna cewa mota ƙirar bas ce ta ƙwace ta buga wani Keke Napep sannan ta ci karo da babbar motar.
Sakamakon haka, direban bas ɗin, Ibrahim Makeri, tare da fasinjoji biyu; Adamu Isiya da Alhaji Shaibu sun rasu nan take.
Daga baya kuma wani daga cikin waɗanda suka ji rauni ya rasu, wanda ya kawo adadin waɗanda suka mutu zuwa huɗu.
An kai gawarwakin da kuma waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Gashuwa da ke Ƙaramar Hukumar Bade.
Likitoci suka tabbatar da mutuwar waɗanda suka rasu, sauran kuwa suna samun kulawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hatsarin mota waɗanda suka
এছাড়াও পড়ুন:
Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano
Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama gungun wasu mutane da ake zargi da safarar mata zuwa kasar Saudiyya.
Hisbah ta dakile yunkurin mutanen ne a yayin da suke kokarin safarar wasu mata hudu daga jihohin Kano da Jigawa da Yobe, ta hannun wakilansu da ke sassan kasashen Yammacin Afirka?
Mataimakin Babban Kwamnand Hukumar, Dakta Mujahideen Aminudeen, ya ce masu safarar matan sun yaudarin matan da aka ceto cewa za su yi musu biza zuwa kasar Ghana inda daga nan za su wuce da su zuwa Saudiyya domin sama musu ayyukan yi.
An kana daya daga cikin mutanen ne a ranar Lahadi, wanda hakan ya kai ga cafke shugabansu da ake kira Bashir Sani Ibrahim.
Ballon d’Or: Wa zai lashe kyautar 2025? Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyu NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen MalabuUku daga cikin matan masu shekaru 30 sn fito ne daga jihohin Kano da Jigawa a yayin da hudun mai shekara 35 da fito daga Jihar Yobe.
Dakta Aminudeen ya bayyana cewa matan sun biya mutanen Naira milian bibbyu, za su ciko Naira miliiyan 1.5 kowannensu domin sama musu biza.
Ya ce, “Wannan shi ne abin da muke ta gargadin mutane a kai — kar a yarda da tafiya ba tare da sanin inda za a kai su ba. Ana yaudarar mutane, ana kwace musu kuɗinsu, kuma da zarar sun isa ƙasashen waje ana tilasta musu shiga harkar karuwanci, fataucin miyagun ƙwayoyi ko kuma tsunduma cikin rayuwar kunci.”
Ya shawarci ’yan Najeriya da su guji irin waɗannan haɗurran tafiya, yana mai jaddada cewa kuɗin da ake ɓatawa wajen irin wannan safarar ya fi dacewa a saka shi a harkokin kasuwanci a gida.
“Da naira miliyan biyu ko uku da rabi, mutum zai iya fara kasuwanci mai kyau a Najeriya maimakon fadawa tarkon waɗannan miyagun dabaru,” in ji shi.
Ya nuna godiya cewa an samu damar dakile wannan yunkuri, yana mai cewa da masu safarar mutanen sun ci nasara, da lallai matan sun ɓace ba tare da sahu ba.
“Mun tattara bayanansu da fasfofonsu muka mika su ga Hukumar Yaƙi da Safarar Mutane (NAPTIP). Za mu ci gaba da sa ido har sai an kammala bincike kan lamarin,” in ji shi.