Aminiya:
2025-11-08@14:22:37 GMT

Sanata Natasha ta koma Majalisar Dattawa

Published: 23rd, September 2025 GMT

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan mai wakiltar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawa, ta koma ofishinta da ke harabar majalisar bayan ƙarewar wa’adin dakatarwar watanni shida da aka yi mata.

A wani bidiyon komawarta ofis da ya karaɗe shafukan sada zumunta, ’yar majalisar ta zargi Shugaban Majalisar Dattawan, Sanata Godswill Akpabio da ɗaukarta a matsayin baiwarsa.

Yarima Salman ya jagoranci jana’izar babban mai ba da fatawa na Saudiyya Kotu ta hana NUPENG rufe Matatar Ɗangote

A cewarta, kamar yadda Akpabio ke matsayin sanata haka ita ma sanata ce.

Sanata Natasha ta ce duk da cewa an dakatar da ita ba bisa ƙa’ida ba, ta riƙa sauke nauyin al’ummar mazaɓarta na Kogi ta Tsakiya, saboda a cewarta ba ta son al’ummarta su ji kamar an yi watsi da su.

Tun da safiyar yau ce rahotanni suka bayyana cewa an buɗe ofishin sanatar da ke Suite 2.05 a cikin ginin Majalisar Dattawan.

Gabanin komawarta, ’yan sanda sun yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa magoya waɗanda suka raka ta zuwa Majalisar Dattawa daga Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.

Bayanai sun ce magoya bayan sun yi tattaki ne domin raka sanatar zuwa majalisar domin komawa bakin aikinta.

Ana iya tuna cewa mako gabanin komawarta ne Sanata Natasha ta rubuta wa Majalisar Dattawan wasiƙa, wadda ta bayyana a niyyarta ta dawowa aiki bayan dakatarwa na tsawon wata shida, amma majalisar ta ce ta ɗan jira tukuna.

A watan Fabrairu ne dai tankiya ta ɓarke a zauren Majalisar Dattawa tsakanin shugaban majalisar da Sanata Natasha, lamarin dai ya kai ga har Akpabio ya umarci ɗaya daga cikin masu yi wa sandan majalisar hidima da ya fitar da ita daga zauren majalisar, kuma daga bisani aka dakatar da ita na tsawon wata shida.

Wannan lamarin ya kai ga har Sanata Natasha ta yi kira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da ta hukunta Majalisar Dattawan Najeriya game da dakatarwar da aka yi mata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa a Majalisar Dattawa Majalisar Dattawan majalisar da

এছাড়াও পড়ুন:

Putin : zamu dauki mataki idan Amurka ta koma gwajin makaman nukiliya

Shugaban Rasha Vladimir Putin ya yi gargadin cewa Moscow za ta dauki “matakan mayar da martani” idan Amurka ta koma gwada makaman nukiliya, a yayin da ake kara samun takun saka tsakanin manyan kasashen biyu masu makamman nukiliya.

A yayin wani taro da ya yi da Majalisar Tsaron Rasha a ranar Laraba, Putin ya umarci Ma’aikatar Harkokin Waje, Ma’aikatar Tsaro, hukumomin leken asiri, da su tantance yiwuwar sake fara gwaje-gwajen makamman nukiliya da kuma gabatar da shawarwari don matakan farko.

“Dangane da wannan batu, ina umurtar ma’aikatun dasu gabatar da shawarwari kan matakan farko da za su iya mayar da hankali kan shirye-shiryen gwaje-gwajen makaman nukiliya,” in ji Putin.

Umarnin da ya bayar ya nuna martani ne ga umarnin da shugaban Amurka Donald Trump ya bayar a ranar 30 ga Oktoba na cewa Washington za ta koma gwajin makamman nukiliya, wanda hakan ya kawo karshen dakatar da gwaje-gwajen irin wadanan miyagun makamai da aka yi tun 1992.

Trump ya yanke wannan shawara ne ‘yan kwanaki bayan ya la’anci Moscow saboda gwajin sabon makami mai linzami na Burevestnik, makamin da ke amfani da makamashin nukiliya wanda zai iya ɗaukar makamin nukiliya.

Rasha ba ta yi wani gwajin nukiliya ba tun bayan rugujewar Tarayyar Soviet a 1991, amma Kremlin yanzu ta nuna cewa za ta iya sake duba wannan matsayin idan Amurka ta fara.

kasashen Rasha da Amurka su ne manyan kasashen duniya masu karfin nukiliya, inda na farko ke da kusan makamin kare dangi 5,459, na biyu kuma ya kai kimanin makamin kare dangi 5,177.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran, China da Rasha sun tattauna gabanin taron Kwamitin Gwamnonin IAEA November 6, 2025 Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho November 6, 2025 Najeriya Ta Sake Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar November 6, 2025 Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya November 6, 2025 Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba November 6, 2025 Masu Sa Ido na Tarayyar Afirka: Zaben Tanzania Ya Keta Ka’idojin Demokradiyya November 6, 2025 An Kama ‘Yan Jarida 3 A Nijar Bisa Tuhumar  Fitar Da Bayanai Na Hukuma November 5, 2025 Sudan Ta Sake Jaddada Tuhumar Kasar UAE  Da Taimakon Rundunar RSF November 5, 2025 Shugaban Mali Ya Yi jawabi Akan Hana Shigar Da Man Futur Da Masu Ikirarin  Jihadi Suke Yi November 5, 2025 Iran : bisa sharadi ne muka saki ‘yan Faransa daga gidan yari November 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanata Barau Zai Yi Ƙarar Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
  • Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah
  • Putin : zamu dauki mataki idan Amurka ta koma gwajin makaman nukiliya
  • Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu
  • Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu
  • Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai
  • Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu