Wata mata ta ƙone fuskar ’yar mijinta da tafasasshen man girki a Borno
Published: 20th, September 2025 GMT
Wata matar aure ta shiga hannu kan zargin ƙone fuskar ’yar mijinta, Fatima Talba mai shekara 17 da tafasasshen man girki, a unguwar Jiddari Polo da ke Jihar Borno.
Wata majiya ta tabbatar da cewa lamarin ya faru a ranar Asabar da ta gabata, bayan wata taƙaddama da kaure tsakanin Fatima da matar ubanta.
“Matar ce ta kwara wa Fatima man girki mai zafi a fuska, wanda ya janyo mata mummunan ƙuna,” in ji majiyar.
An bayyana cewa Fatima na tare da mahaifinta a lokacin da suke shirye-shiryen aurenta da ake sa ran yi a nan gaba.
Bayan faruwar lamarin, an garzaya da ita Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), inda ta ke kwance a sashen kulawa ta musamman.
“Halin da Fatima ke ciki ya tsananta, fuskarta ta ƙone sosai,” cewar majiyar.
Kakakin rundunar ’yan sandan Borno, Nahum Dado, ya tabbatar da cewa an kama matar da ake zargi da aikata laifin.
Jama’ar unguwar sun tausaya w Fatima baya tare da kira ga hukumomi da su tabbatar da an yi mata adalci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda matar aure
এছাড়াও পড়ুন:
GORON JUMA’A 19-09-2025
Ina gaida Mahaifiyata da Mahaifina, Hajiya Saratu da Alhaji Aliyu Minjibir. Sai Gidana Alhaji Musa Yusuf, sai aminiyata Hajiya Kubra Bashir Abdullahi, sai Ƴa ta Mariya, da ƙannena Rashida Aliyu Minjibir, Zainab Aliyu Minjibir, Aliya Aliyu Minjibir, Aliyu Aliyu, Abubakar Aliyu Minjibir Muhammad Aliyu Minjibir, da fatan sun yi juma’a lafiya.
Saƙo daga Maryam M. Aminu
Saƙon gaisuwata zuwa ga Babata da Babana, sai ƙawayena kamar su; Nawal, Zee-zee Kwalale, Halima Saleh, Fatima Kabir, Maryam Isma’il (Namesake), Keleri. Sannan ƴ an’uwana Yaya, Muhammad, Iman, Al-Amin(TK), Ummulkhurthum, Jawad, Zainab Aminu, Abba, Abdulrahman, Jawahir, Fatima.
Saƙo daga Muhammad Abdullah, Unguwar Fagge Jihar Kano:
Ina gaishe da mahaifiyata da mahaifina dan ba zan fara ba sai na fara da su, sannan ina gaishe da ƴ ar’uwata rabin rai, sai abokaina, da ƴ an’uwan mahaifiyata da ƴ an’uwan mahaifina, da abokaina Aliyu, Aliyu A., Sultan, Ahmad Ghali, Amir, Iman, Ummussalama Abdulrasheed, Hajiya, Siyama, Usman Nasir, Abdulrahman Abdulrashid, Abdulsamad Abdullahi, da atan sun yi juma’a lafiya.
Saƙo daga Chef Maryam (C.E.O Meerah’s Culinary Art Bakery), daga Jihar Kano:
Saƙon gaisuwa ta musamman ga ƴ an’uwana musulmi na faɗin duniya. Sannan ina gaida iyayena sai ɗalibaina, ƙawayena da abokan aikina, kamar su; Fatima Jamilu (Nahnah’s Kitchen), Aisha Kamaluddeen (Princess Ayesha), Rukayya Muhammad Isah, Serah Johnson, Khadija Abdulhadi (Chef Dija/Dijah local Candies), Umaima Sani, Wasila Bello Umar, Dr. Hauwa Aliyu Kaita, Nr. Mrs. Fa’iza Uthman, Nafisa Omar Yahaya (Chef Omson), Dt. Maryam, Ms. Esther Samuel, Dr. Sanaya, Salma M. Rahim, Fauziyya Bukar (Fabz Delight), Asiya Khalil, Dr. Maryam A. A. Phd., Ed. Muhammad Al-amin, Kubra Auwal Yakub (African spices by Chef Hadizat), Hajiya Aisha Jabi, Halima Muhammad Dikko, Acnt. Zakiyya Habib da sauransu. Da fatan suna nan lafiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp