Mun ci ribar Naira biliyan 601 a watanni shidan farkon 2025 – Bankin GT
Published: 24th, September 2025 GMT
Kamfanin GTCO, mamallakin bankin GT, ya bayyana samun ribar Naira biliyan 601 a watanni shida na farkon shekarar 2025.
Sai dai bankin ya ce duk da haka ribar tasa raguwa ta yi a kan ta Naira tiriliyan daya da ya ci a farkon shekarar da ta gabata.
Kotun Indiya ta daure dan Najeriya shekara 10 kan safarar miyagun kwayoyi DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya KamataWannan na kunshe ne a cikin sakamakon binciken kudi kamfanin ya fitar, wanda ya ƙare ranar 30 ga Yuni, 2025.
Bankin ya kuma ce amma ribar kafin a cire haraji ce, idan aka cire kuma za ta koma biliyan 449.01, idan aka kwatanta da biliyan 905.57 a daidai wannan lokaci na shekarar 2024.
Duk da raguwar kudaden shiga, hukumar gudanarwar bankin ta amince da biyan ribar Naira 1.00 ga duk masi hannun jari a cikinsa, kamar yadda aka yi a rabin farko na 2024.
Za a biya wannan ribar ce ga masu hannun jari da sunayensu ke cikin rajistar mambobi a ranar 7 ga Oktoba, 2025.
Sai dai ribar kamfanin ta ragu da kashi 43.5 cikin 100 a zangon farko na 2025 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, sakamakon faduwar darajar daga kadarorin kudi kamar takardun bashi da takardun baitul-mali.
Ribar da ba a tabbatar ba daga darajar kadarorin kudi na bankin, wanda yawancin kadarorinsa ke cikin takardun kudi fiye da rance ga abokan ciniki, ta fadi zuwa Naira biliyan 1.5 daga Naira biliyan 331.6.
Wannan ya haifar da raguwar sauran kudaden shiga, wanda shi ne ginshiƙin kudaden shiga na kamfanin a bara, da kashi 91.8 cikin 100.
Jimillar kudaden shiga na bankin ya fadi zuwa Naira biliyan 523.2 daga Naira biliyan 680.5 a cikin wannan lokaci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Naira biliyan
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan
A yau Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jaddada bukatar gina ingantaccen yankin ciniki cikin ’yanci na tashar ruwa ta Hainan ko FTP a takaice. Shugaba Xi ya bayyana bukatar ne yayin dake sauraron rahoton aiki game gina yankin na FTP a birnin Sanya na lardin Hainan dake kudancin kasar Sin.
A cewarsa, gina yankin FTP na Hainan muhimmiyar manufa ce ta kwamitin kolin JKS, wadda aka tsara domin zurfafa cikakkun sauye-sauye, da bude kofa ga waje a sabon zamani.
Shugaban na Sin ya kara jaddada bukatar kyautata nazari, da aiwatar da ka’idojin aiki na cikakken zama karo na hudu na kwamitin kolin JKS na 20, tare da kokarin cimma burikan da aka sanya gaba, dangane da bunkasa yankin FTP na Hainan a dukkanin fannoni, ta hanyar lura da tsare-tsare, da aiki tukuru da wanzar da kwazon aiki.
A ranar 18 ga watan Disamban bana ne yankin FTP na Hainan, zai kaddamar da ayyukan kwastam na musamman na daukacin tsibirin, matakin da shugaba Xi ya ce zai kasance jigon matakai da kasar Sin za ta aiwatar, don fadada bude kofa mai inganci, da ingiza gina budadden tattalin arzikin duniya. (Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA