Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta SERAP tare da Amnesty International sun nemi Shugaba Bola Tinubu ya janye ƙarar da aka shigar a kotu kan ɗan gwagwarmaya Omoyele Sowore, da kuma kamfanonin sada zumunta X da Facebook. Ƙungiyoyin sun bayyana damuwa cewa hukumomin tsaro na ƙara amfani da kotu wajen tsoratar da ƴan Nijeriya da hana su faɗar albarkacin baki.

A cikin wata wasiƙar da suka aike wa shugaban ƙasa ranar 20 ga Satumba, 2025, SERAP da Amnesty sun bayyana cewa ƙarar da DSS ta shigar bisa zargin saƙonnin da ake cewa sun na adawa da Tinubu ya zama wani SLAPP (ƙarar da ake amfani da ita don toshe bakin masu suka). Sun ce irin waɗannan suna haifar da tsoro da hana ƴancin faɗar albarkacin baki da musayar bayanai a cikin al’umma.

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

Ƙungiyoyin sun buƙaci shugaban ƙasa ya umarci Ministan Shari’a kuma AGF, Lateef Fagbemi (SAN), ya gaggauta janye ƙarar tare da gabatar da dokar hana SLAPP a gaban majalisar dokoki. Sun ce hakan zai kare ƴan ƙasa daga amfani da kotu wajen take ƴanci tare da tabbatar da ƴancin faɗar albarkacin baki da suka ce ginshiƙi ne na kowace dimokuraɗiyya.

Sun kuma yi gargadin cewa idan gwamnatin Tinubu ba ta janye ƙarar cikin kwanaki 7 ba, za su kai ƙarar gaban Kotun ECOWAS. SERAP da Amnesty sun jaddada cewa ƴancin faɗar albarkacin baki haƙƙi ne na kowa, kuma ƴan siyasa, musamman shugabanni, ya kamata su ɗauki suka da adawa a matsayin wani ɓangare na rayuwar dimokuraɗiyya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: SERAP faɗar albarkacin baki

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Mali Ya Yi jawabi Akan Hana Shigar Da Man Futur Da Masu Ikirarin  Jihadi Suke Yi

Shugaban kasar Mali Assimi Goita ya yi wa al’ummar kasar jawabi akan karancin man fetur da ake fama da shi a kasar da kuma yadda masu ikirarin Jihari suke killace motocin dakon makamashi.

An fara samun kamfar man fetur ne a kasar Mali wacce ba ta da iyaka ruwa, da masu ikirarin jihadi su ka tare kan iyaka da hana tankokin man fetur shiga cikin kasar.

Goita ta bayyana cewa:

“ A duk lokacin da za a dauko motocin dakon mai, mutane suna mutuwa, ana yin kwanton bauna akan hanya,ana kona motocin da mutane a cikinsu har su kone kurmus.”

Goita ya bayyana haka ne a lokacin dake halartar bikin bude wurin hako ma’adanin “Lithium” a yankin Bougouni a kudancin kasar.

Kungiyar Jama’at Nusrat al-Islam Wal-Muslimin mai alaka da alka’ida ce take killace tankokin dakon man fetur da hana su zuwa gidajen mai.

Tun a cikin watan Satumba ne dai kungiyar mai dauke da makamai ta sanar da hana shigar da tankokin man fetur cikin kasar.

Sojojin kasar ta Mali dai suna yi wa tankokin jigilar man fetur rakiya daga kan iyaka har zuwa birnin Bamako, tare da yin amfani da jiragen yaki domin kai wa masu dauke da makaman hari.

Shugaban kasar ta Mali ya kira yi al’ummar kasar da su rage gudanar da tafiye-tafiye domin rage karfin tasirin kamfar man fetur din.

A cikin birnin Bamako ana ganin dogayen layukan ababan hawa a cikin gidajen man fetur.

Tun bayan juyin mulki a kasar, karancin man fetur din yana a matsyain koma baya mafi girma da kasar take fuskanta.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran : bisa sharadi ne muka saki ‘yan Faransa daga gidan yari November 5, 2025 Gaza : MDD Ta damu kan keta yarjejeniya tsagaita wuta da Isra’ila ke yi  November 5, 2025 Kungiyoyin agaji sun ce tallafin da ake bai wa Gaza bai isa ba November 5, 2025 China ta yi alkawarin ci gaba da tallafawa Najeriya bayan barazanar Trump November 5, 2025 Imam Khamenei: Rikici Tsakanin Iran da Amurka na asasi ne November 5, 2025 Iravani: Kalaman Trump barazana ne ga zaman lafiyar duniya November 5, 2025 Khatibzadeh: Shirin Nukiliyar Iran ne aka fi maganarsa a duniya November 5, 2025 An zabi Mamdani musulmi na farko a matsayin Magajin Garin birnin New York na Amurla November 5, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Batun Tura Sojojin Kasashen Waje Zuwa Gaza November 5, 2025 Iran Da Pakistan Sun Kulla Yarjeniyoyi Guda Biyar Kan Harkar Sadarwa Da Al’adu November 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanata Barau Zai Yi Ƙarar Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Tarayyar Afirka Ta Yi Kiran Da A Girmama ‘Yancin Kai Na Najeriya Da Rashin Tsoma Baki A Harkokin Gidanta
  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Mun sami gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro
  • Shugaban Kasar Mali Ya Yi jawabi Akan Hana Shigar Da Man Futur Da Masu Ikirarin  Jihadi Suke Yi