SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook
Published: 21st, September 2025 GMT
Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta SERAP tare da Amnesty International sun nemi Shugaba Bola Tinubu ya janye ƙarar da aka shigar a kotu kan ɗan gwagwarmaya Omoyele Sowore, da kuma kamfanonin sada zumunta X da Facebook. Ƙungiyoyin sun bayyana damuwa cewa hukumomin tsaro na ƙara amfani da kotu wajen tsoratar da ƴan Nijeriya da hana su faɗar albarkacin baki.
A cikin wata wasiƙar da suka aike wa shugaban ƙasa ranar 20 ga Satumba, 2025, SERAP da Amnesty sun bayyana cewa ƙarar da DSS ta shigar bisa zargin saƙonnin da ake cewa sun na adawa da Tinubu ya zama wani SLAPP (ƙarar da ake amfani da ita don toshe bakin masu suka). Sun ce irin waɗannan suna haifar da tsoro da hana ƴancin faɗar albarkacin baki da musayar bayanai a cikin al’umma.
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan TinubuƘungiyoyin sun buƙaci shugaban ƙasa ya umarci Ministan Shari’a kuma AGF, Lateef Fagbemi (SAN), ya gaggauta janye ƙarar tare da gabatar da dokar hana SLAPP a gaban majalisar dokoki. Sun ce hakan zai kare ƴan ƙasa daga amfani da kotu wajen take ƴanci tare da tabbatar da ƴancin faɗar albarkacin baki da suka ce ginshiƙi ne na kowace dimokuraɗiyya.
Sun kuma yi gargadin cewa idan gwamnatin Tinubu ba ta janye ƙarar cikin kwanaki 7 ba, za su kai ƙarar gaban Kotun ECOWAS. SERAP da Amnesty sun jaddada cewa ƴancin faɗar albarkacin baki haƙƙi ne na kowa, kuma ƴan siyasa, musamman shugabanni, ya kamata su ɗauki suka da adawa a matsayin wani ɓangare na rayuwar dimokuraɗiyya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: SERAP faɗar albarkacin baki
এছাড়াও পড়ুন:
Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin – ACI
Ya gargadi cewa, tarihi ba zai gafarta wa shugabannin Arewa ba idan suka kasa daukar matakin gaggawa wajen dakile kashe-kashe, garkuwa da mutane da rikice-rikicen da ke addabar yankin. Ya ce shiru da fifita wasu akan wasu daga cikin shugabanni suna kara ta’azzara matsalar tsaro a jihohin Zamfara, Kaduna, Katsina, Filato da Benuwe.
Ya bayyana cewa akwai damuwa matuka yayin da ‘yan bindiga ke ci gaba da addabar al’umma, wasu daga cikin manyan mutane na fifita shirya shagulgula masu tsada maimakon kiraye-kirayen tarurrukan neman mafita na gaske don kawo karshen wannan rikici.
“Lokacin yin shiru ya wuce, yanzu ne lokacin daukar mataki. Tarihi ba zai gafarta wa halin ko-in-kula ba a lokacin da ake bukatar mataki fiye da kowane lokaci.”
Idris ya ce kungiyarsu na cikin damuwa matuka bisa abin da ya kira “ƙin ɗaukar mataki na gaggawa daga hukumomin tsaro duk da bayanan sirri da ke hannunsu, lamarin da ya bar gwamnonin jihohi cikin wahala da kuma barin ‘yan kasa cikin hali na shakku da rashin tsaro:.
Ya kuma bukaci ‘yan Arewa da su kaurace wa rarrabuwar kawuna, yana mai jaddada cewa tsawon ƙarnuka mutane masu bambancin addinai da kabilu sun zauna tare cikin zaman lafiya.
Har ila yau, dole ne a fahimci zaman lafiya ba wai kawai rashin rikici ba ne, har da nufin kasancewar adalci, da mutunci ga kowa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp