Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?
Published: 21st, September 2025 GMT
A ɓangare ɗaya kuma Turkiyya na ƙara nuna damuwa bayan harin da Isra’ila ta kai a birnin Doha.
Mai magana da yawun ma’aikatar tsaro ta Turkiyya, Rear Admiral Zeki Akturk ya yi gargaɗin cewa “Isra’ila za ta iya faɗaɗa hare-harenta baya ga Ƙatar. Za ta iya ingiza yankin baki ɗaya cikin bala’i.”
Mece ce shawarar da Masar ta bayar?
Shawarar da Masar ta bayar ya ƙunshi samar da tsarin haɗe ayyukan sojin ƙasa da na sama da cibiyoyin tsaro, tare da haɗe cibiyoyin horaswa da ayyukan soji.
Haka nan kuma ƙasashen ne za su yanke hukunci kafin amfani da dakarun bayan tattaunawa a tsakaninsu.
Kafar yaɗa labarai ta Al Akhbar da ke Lebanon ta ce a ƙarƙashin tsarin, Masar ta ce za ta samar da dakaru 20,000, sannan Saudiyya za ta zamo ta biyu mafi bayar da gudumawa.
Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi ya tattauna da ƙasashe da dama a kan wannan batu, kuma akwai yiwuwar harin da Isra’ila ta kai a Doha zai iya farfaɗo da maganar.
An taɓa samun irin wannan ƙawance a lokuta daban-daban tsakanin ƙasashen yankin, kamar a lokacin yaƙin yankin Gulf da kuma yaƙe-yaƙen da aka yi a Isra’ila.
An taɓa ƙulla irin wannan ƙawancen tsaro a baya tsakanin ƙasashen Larabawa da na Musulmi wadda ake kira ‘Central Treaty Organisation’, wadda aka yi wa laƙabi da Yarjejeniyar Baghdad. Yarjejeniyar ta yi aiki daga shekara ta 1955 zuwa 1979.
Ƙasashen Larabawa sun yi mummunar suka kan harin da Isra’ila ta kai a Ƙatar
Firaiministan Iraƙi Mohammed Shia al-Sudani ya kuma yi kira da a samu ‘ƙawancen soji na ƙasashen Musulmai’.
Kafar yaɗa labarai ta Turkiyya, TRT World, ta ambato shi na cewa akwai buƙatar ɗaukar mataki na bai-ɗaya kan abubuwan da Isra’ila ta aikata a Gaza da kuma Ƙatar a baya-bayan nan.
Al-Sudani ya ce harin da Isra’ila ta kai a Doha, wanda ya kashe mambobin Hamas biyar da wani babban jami’in tsaron Ƙatar “taka dokokin duniya ne mai matuƙar mamaki” kuma tunatarwa ce kan cewa abubuwan da Isra’ila ke aikatawa barazana ce ga tsaron ɗaukacin yankin.
”Babu wani dalili da zai hana ƙasashen Musulmai haɗa kai domin samar da ƙawancen soji guda ɗaya domin kare kansu,” kamar yadda ya shaida wa tashar talabijin ta Al Jazeera, inda ya buƙaci ƙasashen Larabawa da na Musulmai su samar da haɗaka ta siyasa da tsaro da kuma tattalin arziki.
Ya kamata a hukunta Isra’ila – in ji Ƙatar
“Lokaci ya yi da duniya za ta kawo ƙarshen baki biyu da ake yi sannan a hukunta Isra’ila kan laifukan da ta tafka,” in ji ministan harkokin waje na Ƙatar, gabanin taron da ƙasashen suka yi a ranar Litinin, kamar yadda sashen BBC Persia ya ruwaito.
Ya ce “Ya kamata Isra’ila ta sani cewa wannan yaƙi da take da ƴ an’uwanmu, Falasɗinawa, da nufin korar su daga ƙasarsu, ba zai yi nasara ba.”
Ƙatar ta yi martani da kakkausan harshe bayan harin da Isra’ila ta kai mata ranar 9 ga watan Satumba, kuma ta jaddada cewa yanzu a shirye take kan ko ma mene ne zai faru.
Ɗaya daga cikin manyan jami’an Hamas, Bassem Naim, ya ce ƙungiyar na fatan cewa za a samu “wani ƙwaƙƙwaran mataki na bai-ɗaya daga ƙasashen Larabawa da na Musulmai” kan Isra’ila.
Amurka na da sansanin sojin samanta mafi girma a faɗin Gabas ta tsakiya ne a Ƙatar. Baya ga haka, Ƙatar ta taka muhimmiyar rawa wajen tattaunawar sulhu tsakanin Amurka da Masar da kuma Isra’ila da Hamas.
Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio wanda ya kai ziyara Isra’ila, ya nuna fushinsa kan harin da Isra’ila ta kai a Ƙatar, sai dai ya bayyana cewa wannan ba zai lalata kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin Amurka da Isra’ila ba.
Dama dai akwai ruɗani kan abin da mai magana da yawun fadar shugaban Amurka ta White House, Caroline Leɓitt ta ce game da bayanin da aka yi wa Ƙatar kan harin. Fadar White House ta ce ‘an sanar da Ƙatar kafin kai harin’, sai dai Firaiminstan Ƙatar ya ce ya ‘samu bayanin ne minti 10 bayan kai harin’.
Shin abu ne mai yiwuwa ƙasashen Larabawa su kafa ƙawance kamar NATO?
Batun kafa ƙawancen soji tsakanin ƙasashen Larabawa, mai kama da ƙawancen NATO, abu ne da ya daɗe, sai dai masana ba su da ƙwarin gwiwar cewa abu ne da zai yiwu.
Premanand Mishra, malami a cibiyar zaman lafiya da warware rikice-rikice ta Nelson Mandela a jami’ar Jamia Millia Islamia da ke Indiya, ya ce “An taɓa tattaunawa kan kafa ƙungiyar NATOn Larabawa, kuma Saudiyya ta bai wa batun muhimmanci sosai. Har ma an taɓa naɗa tsohon babban hafsan soji na Pakistan, Raheel Sharif a matsayin shugabanta, to amma sai batun ya gaza ci gaba.”
Ya ce “Muradun tsaro na dukkanin ƙasashen sun sha bamban ta yadda zai yi wahala a samu matsaya ɗaya a tsakaninsu.
Misali, Saudiyya da Iran za su iya watsi da bambance-bambancen da ke tsakaninsu? Domin idan har za a yi haɗakar soji, to akwai buƙatar yin musayar bayanan sirri.”
Duk da cewa akwai ƙoƙarin da aka yi a baya-bayan man na sulhuntawa tsakanin Saudiyya da Iran, babu tabbas kan ko an cimma wata matsaya mai ƙwari da za ta ita samar da ƙawance tsakanin ƙasashen yankin.
Premanand Mishra ya ce wannan shawara ta ƙawancen soji ta samo asali ne daga Masar, abin da ya rage shi ne a ga ko akwai ƙwaƙwarar aniyar aiwatarwa. Sannan kuma ko ƙasashen Yamma, musamman Amurka da ƙawancenta na NATO za su bari a aiwatar da shawarar”
Ya ce tabbas akwai batun kafa NATOn Larabawa a baya, kuma za a ci gaba da samun irin wannan batu a nan gaba, amma akwai shakku kan ko za a iya aiwatarwa.
Dr Mudassir Ƙamar, ƙaramin farfesa a Cibiyar nazarin yankin yammacin Asia a jami’ar Jawaharlal Nehru da ke birnin Delhi na Indiya, ya ce ƙasashen Larabawa na da ƙungiyoyi da dama da suka haɗu a ciki, kamar ƙungiyar Arab League, da OIC da kuma GCC.
Bayan haka akwai dakarun yaƙi da ta’addanci da ke ƙarƙashin jagorancin Saudiyya, to amma matsalar ita ce yadda za a warware matsalolin da ke tsakanin ƙasashen na Larabawa.
Mudassir Ƙamar ya ce “zai yi matuƙar wahala Isra’ila, wadda yanzu ba ta shiri da ƙasashen Larabawa da dama ta kawar da kai daga duk wani yunƙuri na samar da irin wannan ƙawance.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: harin da Isra ila ta kai a ƙasashen Larabawa da ƙawancen soji da ƙawance irin wannan
এছাড়াও পড়ুন:
Zan ci gaba da siyasa har ƙarshen rayuwata – Shekarau
Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau, ya ce zai ci gaba da yin siyasa matuƙar yana numfashi a doron duniya.
Shekarau ya bayyana cewar siyasa wata babbar hanya ce ta hidima wa jama’a.
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Don Yaki da Laifuffuka A Maiduguri Abba ya yaba wa sojoji kan hallaka ’yan bindiga 19 a KanoYayin da yake hira da ’yan jarida a Kano a yayin bikin zagayowar ranar haihuwarsa na cika shekaru 70, Shekarau, inda ya ce gina siyasarsa ne bisa tafarkin addini da ɗabi’a.
“Siyasata addinina ce, addinina kuma siyasata ce. Shiga cikin tsarin samar da shugabanni na gari masu gaskiya hidima ce ga jama’a kuma wannan ibada ce a Musulunci,” in ji shi.
Tsohon gwamnan ya bayyana cewa, siyasarsa ba ta da nasaba da son kai, sai dai niyyar ganin an samar da shugabanni masu adalci da kishin al’umma.
“Matukar ina da ƙarfi, zan ci gaba da bayar da gudunmawa. A gare ni siyasa ba aiki ba ne da ake daina yi; nauyi ne na rayuwa gaba ɗaya,” in ji shi.
Shekarau, wanda ya mulki Jihar Kano daga 2003 zuwa 2011, ya yi kira ga jam’iyyun adawa da su haɗa kai domin ƙarfafa dimokuraɗiyya.
Ya kuma yi kira ga shugabanni su mayar da hankali kan matsalolin rashin tsaro, talauci da yunwa.
Ya kuma yaba wa jam’iyyar PDP bisa juriyarta inda ya bayyana cewar har yanzu tana taka muhimmiyar rawa a siyasar Najeriya.
Ya kuma yi wa makomar siyasar Najeriya fatan alheri, tare da jadadda cewa zai ci gaba da goyon bayan kowace gwamnati don samar da zaman lafiya da jin daɗin ’yan ƙasa.