NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa
Published: 22nd, September 2025 GMT
Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta ce a karon farko za ta shirya taron zuba jari da samar da masana’antu na Arewacin Najeriya, wanda aka shirya gudanarwa a ranakun 29 da 30 ga watan Satumba a Abuja.
Taron wanda aka shirya tare da hadin gwiwar jihohin arewa 19 da kuma kamfanin raya yankin – NNDC, na da nufin mayar da yankin a matsayin wata cibiya ta samun bunkasar tattalin arziki da habaka masana’antu.
Da yake magana a taron manema labarai da aka gudanar ranar Litinin a Abuja, kakakin kungiyar, Farfesa Abubakar Jika Jiddere, ya bayyana taron a matsayin “kira domin zaburar da tattalin arziki da kuma tsare-tsare na cika alkawarin Arewacin Najeriya.”
Ya ce an tsara taron ne a cikin watanni 18 da suka gabata domin kaddamar da wani shiri na kishin kasa wanda zai karfafa ayyukan ci gaba da bude sabbin kafofin damammanki ga yankin, Najeriya da abokan huldar kasa da kasa.
“Wannan taron ba na siyasa ba ne, yana mai da hankali kan tattalin arziki, kan damammaki, da kuma samar da wadata. Yana da zimmar nuna karfin Arewacin Najeriya da kuma gabatar da hangen nesa na ci gaba, kirkire-kirkire, da haɗin gwiwa. Daga yau, za mu bude sabon babi,” in ji Jiddere.
Da yake yin la’akari da irin gudunmawar da yankin ya bayar a tarihi, ya tuna cewa a shekarun 1960 zuwa farkon 1980, Arewacin Nijeriya ya ba da karfin tattalin arzikin kasa ta hanyar noma, masana’antu, da kasuwanci. “Dalarmu na gyada ya kai sararin sama; auduga, fatu, dabbobi, da ma’adanai masu ƙarfi suna tallafawa masana’antu,” in ji shi.
Duk da haka, ya ce rashin tsaro da rashin zuba jari sun rage ci gaban yankin, wanda ya haifar da rikice-rikice na albarkatu masu yawa da kuma abubuwan da ba a san su ba, “Wannan taron yana manufa juya akalar rikicin zuwa ga damammaki da kuma tabbatar da cewa Arewacin Najeriya ya samu kwarin gwiwa zuwa wani sabon zamani na ci gaba,” in ji shi.
Jiddere ya zayyana ginshiƙai masu mahimmanci guda biyar da yankin yake tutiya da su kamar albarkar ƙasa da noma, manyan ma’adanai, albarkatun ɗan adam, ababen more rayuwa, da masana’antu, waɗanda ke samun tallafi kamar ilimi, kiwon lafiya, gidaje, da fasaha.
Ya nanata cewa Arewacin Najeriya “yana da alaƙa da kasa-wata babbar hanyar shiga Nijar, Chadi, Kamaru, Benin, Mali, da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.”
Ya ƙalubalanci masu ruwa da tsaki da su yi nazari a kan abubuwan da ba za a iya amfani da su a yankin ba, yana mai tambaya, “Ta yaya yankin da ya samar da shugabanni da masu ƙirkire-ƙirkire a duniya, ’yan ƙato da gora irin su Alhaji Aliko Dangote da Amina Mohammed, har yanzu bai nuna cikakken ƙarfin tattalin arzikinsa ba?
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa Dattawan Arewa Arewacin Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Kashim Shettima Ya Isa New York Halartar Taron UNGA Na 80
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya isa birnin New York, Amurka, domin halartar taron babban zauren Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 wanda zai gudana daga ranar Litinin 22 ga Satumba zuwa Lahadi 28, 2025. Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu, zai gabatar da jawabin Nijeriya a gaban zauren, tare da shiga wasu tattaunawa da tarukan a gefe da dama.
Ministan Harkokin Ƙasashen Waje, Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa Nijeriya za ta ci gaba da mara baya ga tsarin haɗin gwuiwa tsakanin ƙasashe, ciki har da yunƙurin samun kujerar dindindin a Majalisar Tsaron MDD bisa matsayar haɗin kan Afrika, wato Ezulwini Consensus. Ya ce Shettima zai kuma bayyana sabbin manufofin Nijeriya na rage hayaƙin da ke gurbata muhalli bisa yarjejeniyar Paris.
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan ManomaA yayin da aka tarɓe shi, Shettima ya samu rakiyar ministoci da gwamnoni ciki har da na Kaduna, Uba Sani, wanda ya ce halartar Nijeriya a UNGA zai ƙara jawo masu zuba hannun jari ga tattalin arzikin ƙasar, musamman a fannin ma’adanai, da noma da ilimin sana’o’in dogaro da kai. Ministan Kasuwanci da Zuba Jari, Dr Olajumoke Oduwole, ta ce Nijeriya za ta yi amfani da taron wajen tallata shirin Nigeria Investment Day, da zai mayar da hankali kan ma’adanai, da sadarwa da kuma fasaha.
Rahotanni sun nuna cewa Shettima zai kuma shiga taron kwamitin zaman lafiya na Tarayyar Afrika, tare da ganawa da shugaban gwamnatin Sudan da sauran manyan jami’ai, domin jaddada matsayar Nijeriya kan rikicin Gabas ta Tsakiya, Sudan da gabashin Kongo. Wannan dai na nuna yunƙurin Nijeriya na ƙara taka rawar gani a harkokin diflomasiyya da ci gaban nahiyar Afrika.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp