Leadership News Hausa:
2025-11-04@10:48:14 GMT

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

Published: 20th, September 2025 GMT

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

A yau Juma’a ne aka rufe taron dandalin tattauna batun tsaro na Xiangshan karo na 12 a birnin Beijing, bayan mahalartansa sun zurfafa tattaunawa karkashin jigon “Mara baya ga odar kasa da kasa da ingiza ci gaba cikin lumana.”

An bude taron ne a ranar Laraba, ya kuma hallara sama da wakilai 1,800, ciki har da jami’an gwamnatoci, da kwararru, da masana da wasu masu sanya ido daga kasashe, yankuna da hukumomin kasa da kasa sama da 100.

Mahalarta taron, sun zanta karkashin jigo daban daban, ciki har da “Gina tsarin adalci da daidaito na shugabancin harkokin tsaron kasa da kasa,” da jigon “Amincewa da juna bisa matsayin koli da hadin gwiwar tsaro a yankin Asiya da Fasifik”. Sai jigon “Odar kasa da kasa da tsaron duniya da samar da daidaito,” da kuma “Gina zaman lafiya na shiyyoyi karkashin tsarin tattaunawa da gudanar da shawarwari.”

Taron ya kuma bayar da damar tattaunawa tsakanin manyan kwararru, da dakarun sojoji da malamai, kana an gudanar da wasu tarukan karawa juna sani na sirri, wanda hakan ya ingiza musayar koyi da juna, da fadada kafofin tattaunawa tsakanin Sin da mahalarta tsaron na sassan kasa da kasa. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan Bayelsa

Jami’an tsaro sun kama wani mutum da wayoyin sata guda 17 da kuma kudi a wurin taron sauyin shkear Gwamna Douye Diri daga Jam’iyyar PDP zuwa APC.

A ranar taron, Gwamna Diri tare da yawancin ’yan majalisar dokokin jihar Bayelsa sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyar PDP zuwa APC, a gaban Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, da wasu gwamnoni da manyan jami’an siyasa na ƙasa.

Shugaban sa-kai na jihar, Doubiye Alagba, wanda ya jagoranci kama wanda ake zargin, ya bayyana cewa an mika mutumin ga jami’an Operation Puff Adder na rundunar ’yan sandan jihar domin gudanar da cikakken bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

A cewar Alagba, wanda ake zargin ya amsa laifinsa, inda ya ce ya shigo daga jihar Ribas ne musamman domin amfani da taron siyasar da aka shirya wajen yin sata.

Karuwanci da zubar da cikin ’yan mata ’yan gudun hijira ya karu a Maiduguri NAJERIYA A YAU: Rashin aikin yi da hanyoyin magance su a Najeriya

Ya ce jami’ansu sun kama shi ne bayan sun lura da motsinsa da ya sa suka zarge shi. Bayan bincike, sai suka gano wayoyi 17, kudi N91,000, da kuma katunan ATM da dama a cikin jaka da yake dauke da ita.

Alagba ya kara da cewa, Francis ya shaida musu cewa yana aiki tare da wasu abokan laifi da suka tsere yayin kamun.

Ya kuma bayyana cewa kafin a kama shi, sun riga sun kwashe sama da N400,000, sannan daya daga cikin wadanda suka gudu yana da karin wayoyi da sauran kayayyakin da suka sace.

Shugaban sa-kai din ya gargadi masu aikata laifuka da su guji shiga Bayelsa, yana mai cewa jami’ansa sun samu horo na musamman kan tattara bayanan sirri, lura da halayen jama’a da kuma tsaron taruka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan Bayelsa
  • Abba ya umarci a riƙa gudanar da taron tsaro a ƙananan hukumomin Kano
  • Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka
  • Turkiyye na karbar taron Kasashen Musulmi Kan Halin Da Ake Ciki A Gaza
  • Iran Ta Karbi Sako Kan Batun Komawa Teburin Tattaunawa Ba Kai Tsaye Ba
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.