An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan
Published: 20th, September 2025 GMT
A yau Juma’a ne aka rufe taron dandalin tattauna batun tsaro na Xiangshan karo na 12 a birnin Beijing, bayan mahalartansa sun zurfafa tattaunawa karkashin jigon “Mara baya ga odar kasa da kasa da ingiza ci gaba cikin lumana.”
An bude taron ne a ranar Laraba, ya kuma hallara sama da wakilai 1,800, ciki har da jami’an gwamnatoci, da kwararru, da masana da wasu masu sanya ido daga kasashe, yankuna da hukumomin kasa da kasa sama da 100.
Mahalarta taron, sun zanta karkashin jigo daban daban, ciki har da “Gina tsarin adalci da daidaito na shugabancin harkokin tsaron kasa da kasa,” da jigon “Amincewa da juna bisa matsayin koli da hadin gwiwar tsaro a yankin Asiya da Fasifik”. Sai jigon “Odar kasa da kasa da tsaron duniya da samar da daidaito,” da kuma “Gina zaman lafiya na shiyyoyi karkashin tsarin tattaunawa da gudanar da shawarwari.”
Taron ya kuma bayar da damar tattaunawa tsakanin manyan kwararru, da dakarun sojoji da malamai, kana an gudanar da wasu tarukan karawa juna sani na sirri, wanda hakan ya ingiza musayar koyi da juna, da fadada kafofin tattaunawa tsakanin Sin da mahalarta tsaron na sassan kasa da kasa. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
An sabunta wannan ƙididdiga kusan shekaru shida kamar yadda ya kamata a yi. Abin da ya kamata mu mai da hankali a kai shi ne, ƙididdiga da bayanai su kasance masu sahihanci kuma a yawaita samun su. “An sabunta ƙididdigar, kuma ya nuna mana ainihin halin da muke ciki. Don haka, duk wani ra’ayi na son zuciya da wani ke ganin ya kamata mu kasance kusa da kashi 30, wannan ra’ayinsu ne kawai. Muhimmin abu shi ne an sabunta ƙididdiga watanni da dama da suka wuce, kuma abin da muke gani yanzu shi ne raguwar hauhawar farashi da ta ci gaba.” Fasua ya kuma ambaci cewa Naira ta samu tagomashi a kwanakin baya kuma farashin mai na hauhawa a kasuwar duniya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp