Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
Published: 24th, September 2025 GMT
A yau Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bukaci hada karfi da karfe wajen gina yankin Xinjiang ya zama mafi kyau a cikin tsarin zamanantar da kasar Sin. Ya bukaci hakan ne yayin da ya gana da wakilai daga dukkan kabilu da sauran fannonin rayuwar al’umma a yankin Xinjiang mai cin gashin kansa na arewa maso yammacin kasar Sin.
Xi, wanda shi ne babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana shugaban kwamitin koli na soja, ya isa birnin Urumqi, babban birnin yankin Xinjiang da safiyar yau, domin halartar bukukuwan cika shekaru 70 da kafuwar yankin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yankin Xinjiang
এছাড়াও পড়ুন:
Abba ya yaba wa sojoji kan hallaka ’yan bindiga 19 a Kano
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yaba wa rundunar sojin Najeriya da sauran jami’an tsaro bisa daƙile hare-haren ’yan bindiga a wasu sassan jihar.
Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar.
Kocin Super Eagle ya lashi takobin lashe kofin nahiyar Afirka Mamdani ya zama Musulmi na farko da ya zama magajin garin New York na AmurkaAbba ya yi wannan yabo ne, yayin da yake karɓar babban kwamandan rundunar soji ta 1, a Hedikwatar Kaduna, Manjo Janar Abubakar Sadiq Muhammad Wase, a fadar gwamnati da ke Kano.
Manjo Janar Wase, ya ziyarci Kano domin duba halin tsaro a ƙananan hukumomin Shanono da Tsanyawa.
Ya bayyana yadda mahaifinsa, marigayi Kanal Muhammad Abdullahi Wase, ya taɓa zama kwamishinan soja na Jihar Kano a shekarar 1994.
“Tun lokacin da na karɓi jagorancin rundunar, na ziyarci wuraren da aka kai hare-hare domin na yaba wa jarumtar sojojimmu,” in ji Janar Wase.
Gwamnan ya gode wa sojoji bisa jajircewarsu, tare da jinjina wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan naɗa sabbin hafsoshin tsaro masu ƙwazo da kishin ƙasa.
Ya bayyana cewa gwamnatin jihar za ta bayar da kyautar motoci ƙirar Hilux guda 10 da babura 60 ga rundunar haɗin gwiwa da ke aiki a yankunan da abin ya shafa.
Haka kuma ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro wajen yaƙi da ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da kuma satar shanu.
Idan ba a manta Aminiya ta ruwaito yadda dakarun soji suka daƙile hari tare da kashe ’yan bindiga 19 a yankin Shanono yayin wani samame da suka kai.