Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Published: 20th, September 2025 GMT
Duk da cewa, Nijeriya ce kan gaba wajen kiwon dabbobi a nahiyar Afirka, amma har yanzu, mahukunta a ƙasar sun gaza gudanar da wani kyakkyawan tsari da kuma samar da kayan aiki wajen samar da kashin na dabbobi, inda rashin hakan ke ci gaba da haifar da damuwa ga waɗanda ke fannin a faɗin ƙasar.
“Nijeriya za ta iya samun daloli masu yawa a kasuwar ta duniya”, a cewar Chuka Mordi Babban Jamie’s kamafanin Ellah Lakes kuma wanda ya kasance ɗaya daga cikin masu goyon bayan ganin ana fitar da kashin dabbobin zuwa kasuwannin duniya, domin yin hada- hadar kasuwancinsa.
“Kashin dabbobin ya kasance ɗaya daga cikin hanyoyin samar da kuɗaɗen shiga, musamman wajen sarrafa kashin dabbobin zuwa takin zamani, domin ƙara inganta ƙasar yin noma da kuma amfanin gonar da aka shuka,” in ji Chuka.
Mordi ya ci gaba da cewa, rashin cin gajiyar da ba a yi na kashin dabbobin a ƙasar nan, hakan na ci gaba da haifar da giɓi ga fannin.
“Akwai buƙatar sassan koyar da darussan aikin noma da ke jami’oin ƙasar nan, su sanya darasin koyar da muhimmancin yin amfani da kashin dabbobin a cikin manhajarsu, domin a bunƙasa fannnin”, a cewar Mordi. Kazalika, ya yi kira ga gwamnati da ta samar da wasu shirye-shirye, musamman domin a ilimantar da manya da ƙananan manoma da kuma ƴ an kasuwa, kan albarkar da ke tattare da kashin na dabbobin.
“Ga ƙasa kamar irin Nijeriya da ke ƙoƙarin ganin ta rage yin dogaro daga fannin man fetur, idan ta mayar da hankali, za ta iya amfana da wannan fannin,” Inji Mordi.
Bugu da ƙari bisa wasu alƙaluma da hukumar kula da ƙididdiga ta ƙasa wato NBS ta fitar sun bayyana cewa, a Afirka ta Yamma, Nijeriya ce, kan gaba da ke da Shanu masu ɗimbin yawa, inda a ƙasar ake kiwata Shanun da yawansu ya kai miliyan 20.79.
Kazalika, ƙasar na da sauran dabbobi dasuka haɗa da, Tumaki da Akuyoyi da sauarsu.
Sai dai, duk irin waɗannan ɗimbin dabbobin da ƙasar ke da su, da kuma kasancewar ƙasar kan gaba wajen albarkatun dabbobi a Afirka ta Yamma, amma mahukuntan ƙasar, sun gaza samar da wani kyakaywan tsari na cin gajiyar da ke tattare da Kashin na dabbobin.
Albarkatun da ke cikin ƙashin dabbobi da Jininsu da kuma kashin nasu, za a iya juwa su zuwa wasu sinadarai da dama.
A cewar hukumar NBS, a kullum a Jihar Legas kaɗai, ana yanka Shanu da yawansu ya kai daga 3,000 zuwa 5,000.
Wannan adadin, ba su daga cikin dubban da aka yankawa, ba tare da yarjewar mahukunatan jihar ba, amma duk da hakan, ba a cin gajiyar alfanun da ke tattare da Kashin na dabbobin.
Sunny Omokaro, shugaban ƙungiyar ma’aikatan mahauta na ƙasa, ya sanar da cewa, wannnan rashin ci gajiyar ta Kashin dabbobin, ya sanya Nijeriya rashin samun damarmaki masu yawa.
“Sarrafa kashin dabbobin, zai taimaka wajen ƙara samar da ayyukan yi da samar da kuɗaɗen shiga“ Sunny ya shaida wa jaridar BusinessDay hakan.
Ya buga misali da ƙashin dabbobin, wanda ya ce; za a iya sarrafa shi zuwa abincin dabbobin da sauransu.
Ya sanar da cewa, rashin samar da kayan aikin sarrafa kashin dabbobin zuwa wasu nau’ika, na ƙara haifar wa fannin wani sabon ƙalubale.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Aika Dalibai 588 Zuwa Jihohin Arewa 13 A Karkashin Shirin Musanya
Gwamnatin jihar Kano ta aika dalibai 588 zuwa jihohin Arewa 13 a karkashin shirin musayar dalibai na shekarar 2025/2026.
An kai daliban zuwa jihohinsu da suka hada da Adamawa, Bauchi, Gombe, Jigawa, Katsina, Kebbi, Taraba, da Nasarawa. Bugu da kari, an kai dalibai daga Yobe, Kaduna, Sokoto, Borno, da Kwara lafiya zuwa inda suke, yayin da wasu dalibai 78 kuma za a kwashe su zuwa jihohin Neja da Benue a ranar 30 ga Satumba, 2025.
Kano dai na daya daga cikin jihohin Arewa 19 da ke halartar wannan shiri, wanda aka tsara shi domin inganta hadin kan kasa, hadewa da fahimtar al’adu tsakanin jahohin mambobin kungiyar.
Da yake jawabi ga manema labarai bayan tafiyar da daliban, kwamishinan ilimi, Dakta Ali Haruna Makoda, wanda Daraktan sa ido da tantancewa, Auwal Muhammad Mustapha ya wakilta, ya jaddada kudirin gwamnati na tabbatar da tsaro da walwalar daliban.
“Mai girma Gwamna, yana ba mu dukkan kayan aiki da tallafin kudi don saukaka ayyukanmu da kuma tabbatar da cewa an kai daliban jihohinsu lafiya,” inji shi.
Dakta Makoda ya kuma yabawa iyaye da masu ruwa da tsaki bisa hadin kai da goyon bayan da suke bayarwa wajen ganin shirin ya samu nasara.
COV/Khadija Aliyu