Duk da cewa, Nijeriya ce kan gaba wajen kiwon dabbobi a nahiyar Afirka, amma har yanzu, mahukunta a ƙasar sun gaza gudanar da wani kyakkyawan tsari da kuma samar da kayan aiki wajen samar da kashin na dabbobi, inda rashin hakan ke ci gaba da haifar da damuwa ga waɗanda ke fannin a faɗin ƙasar.

“Nijeriya za ta iya samun daloli masu yawa a kasuwar ta duniya”, a cewar Chuka Mordi Babban Jamie’s kamafanin Ellah Lakes kuma wanda ya kasance ɗaya daga cikin masu goyon bayan ganin ana fitar da kashin dabbobin zuwa kasuwannin duniya, domin yin hada- hadar kasuwancinsa.

“Kashin dabbobin ya kasance ɗaya daga cikin hanyoyin samar da kuɗaɗen shiga, musamman wajen sarrafa kashin dabbobin zuwa takin zamani, domin ƙara inganta ƙasar yin noma da kuma amfanin gonar da aka shuka,” in ji Chuka.

Mordi ya ci gaba da cewa, rashin cin gajiyar da ba a yi  na kashin dabbobin a ƙasar nan, hakan na ci gaba da haifar da giɓi ga fannin.

“Akwai buƙatar sassan koyar da darussan aikin noma da ke jami’oin ƙasar nan, su sanya darasin koyar da muhimmancin yin amfani da kashin dabbobin a cikin manhajarsu, domin a bunƙasa fannnin”, a cewar Mordi.  Kazalika, ya yi kira ga gwamnati da ta samar da wasu shirye-shirye, musamman domin a ilimantar da manya da ƙananan manoma da kuma ƴ an kasuwa, kan albarkar da ke tattare da kashin na dabbobin.

“Ga ƙasa kamar irin Nijeriya da ke ƙoƙarin ganin ta rage yin dogaro daga fannin man fetur, idan ta mayar da hankali, za ta iya amfana da wannan fannin,” Inji Mordi.

Bugu da ƙari bisa wasu alƙaluma da hukumar kula da ƙididdiga ta ƙasa wato NBS ta fitar sun bayyana cewa, a  Afirka ta Yamma, Nijeriya ce, kan gaba da ke da Shanu masu ɗimbin yawa, inda a ƙasar ake kiwata Shanun da yawansu ya kai miliyan 20.79.

Kazalika, ƙasar na da sauran dabbobi dasuka haɗa da, Tumaki da Akuyoyi da sauarsu.

Sai dai, duk irin waɗannan ɗimbin dabbobin da ƙasar ke da su, da kuma kasancewar ƙasar kan gaba wajen albarkatun dabbobi a Afirka ta Yamma, amma mahukuntan ƙasar, sun gaza samar da wani kyakaywan tsari na cin gajiyar da ke tattare da Kashin na dabbobin.

Albarkatun da ke cikin ƙashin dabbobi da Jininsu da kuma kashin nasu, za a iya juwa su zuwa wasu sinadarai da dama.

A cewar hukumar NBS, a kullum a  Jihar Legas kaɗai, ana yanka Shanu da yawansu ya kai daga 3,000 zuwa  5,000.

Wannan adadin, ba su daga cikin dubban da aka  yankawa, ba tare da yarjewar mahukunatan jihar ba, amma duk da hakan, ba a cin gajiyar alfanun da ke tattare da Kashin na dabbobin.

Sunny Omokaro,  shugaban ƙungiyar ma’aikatan mahauta na ƙasa, ya sanar da cewa, wannnan rashin ci gajiyar ta Kashin dabbobin, ya sanya Nijeriya rashin samun damarmaki masu yawa.

“Sarrafa kashin dabbobin, zai taimaka wajen ƙara samar da ayyukan yi da samar da kuɗaɗen shiga“ Sunny ya shaida wa jaridar BusinessDay hakan.

Ya buga misali da ƙashin dabbobin, wanda ya ce; za a iya sarrafa shi zuwa abincin dabbobin da sauransu.

Ya sanar da cewa, rashin samar da kayan aikin sarrafa kashin dabbobin zuwa wasu nau’ika, na ƙara haifar wa fannin wani sabon ƙalubale.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Barazanar kawo hari abin ɗaga hankali ne ga duk ’yan Nijeriya — Peter Obi

Tsohon ɗan takarar Shugaban Najeriya a jam’iyyar Labour, Peter Obi, ya ce barazanar kawo wa Najeriya hari da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi abin damuwa ne da ke da ɗaga hankalin dukkan ’yan ƙasar.

Tsohon Gwamnan na Jihar Anambra, ya bayyana haka ne cikin wani saƙo da ya wallafa yammacin wannan Litinin a shafinsa na X.

Gidan rediyo ya ɗauki nauyin sanya yara 40 a makaranta a Kano ’Yan Sandan Legas sun ayyana neman Sowore ruwa a jallo

Obi ya bayyana cewa, barazanar turo sojojin Amurka su yaƙi ta’addanci da ma sanya Nijeriya cikin jerin ƙasashen da Amurkan take da damuwa da su, lamari ne da dole dukkan ɗan Najeriya mai son ƙasar ya ja masa hankali.

“Babu shakka Nijeriya na fama da matsalar tsaro, wadda ta yi sanadiyar mutuwar mutane da dama da ma asarar dukiya.

“A cewar Ƙungiyar Amnesty, aƙalla mutum 10,000 aka kashe a Nijeriya daga watan Mayun 2023, kuma kamar yadda na sha nanatawa, kashe-kashe a Najeriya abin takaici ne, kuma abin Allah-wadai da ya zama dole a tashi haiƙan wajen magancewa.”

Obi ya ce za a iya magance matsalar ta hanyar samun shugabanci na nagari, “duk da cewa ba a wannan gwamnatin matsalar ta fara ba, amma akwai rashin ƙwarewa da rashin takaɓus daga ɓangaren wannan mulkin na gwamnatin APC wajen tunkarar matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta.”

Ya ce Najeriya da Amurka suna da tarihin alaƙa da juna mai kyau, “kuma bai kamata a watsar da wannan alaƙar ba a yanzu.

“Wannan sabuwar dambarwar na buƙatar haɗakar diflomasiyya da tattaunawa tsakanin ƙasashen biyu domin lalubo hanyoyin magance matsalar.”

Barazanar da Trump ya yi wa Nijeriya

A bayan nan ne dai Shugaba Trump ya umarci Ma’aikatar Yaƙi ta Amurka ta fara shirye-shiryen yiwuwar kai hari ƙasar, bayan ya yi zargin cewa ana yi wa mabiya addinin Kirista kisan gilla a ƙasar.

Trump ya bayar da umarnin ne a saƙon da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, kwana guda bayan da ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya, ba tare da ya bayyana takamaimai inda ya samu waɗannan alƙaluma ba.

Tinubu ya mayar da martani

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya bayyana cewa tun daga lokacin da gwamnatinsa ta hau mulki a shekarar 2023, tana ci gaba da gudanar da tattaunawa da duka shugabannin Kiristoci da Musulmai domin ƙarfafa haɗin-kai da magance matsalolin tsaro da ke shafar ’yan ƙasa daga kowane yanki da addini.

Tinubu ya ƙara da cewa Nijeriya tana nan daram a matsayin ƙasa mai dimokuraɗiyya, wadda kundin tsarin mulkinta ke tabbatar da ’yancin yin addini.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma
  • Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
  • Barazanar Trump: Ba ma so a ƙirƙiri wata Sudan ɗin a Nijeriya — Tuggar
  • KADUNA TA ZAMA JIHAR FARKO A NIJERIYA DA TA AIWATAR DA SHIRIN SAMAR DA ABINCIN MAI GINA JIKI GA YARA – UNICEF
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Barazanar kawo hari abin ɗaga hankali ne ga duk ’yan Nijeriya — Peter Obi
  • Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT
  • Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi
  • Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza