Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima
Published: 21st, September 2025 GMT
Ya ƙara da cewa, “Ina fatan hakan ba gaskiya ba ne, domin kuwa idan wannan mutum ya zama shugaban INEC, ko shakka babu; wannan gwamnati kai tsaye na gayyato yaƙin Basasa ne.”
Da yake mayar da martani a kan batutuwan da jam’iyyun siyasa suka fara yi na yaƙin neman zaɓe, ya zargi hukumar zaɓe ta ƙasa da gazawa waje aiwatar da dokokin yaƙin neman zaɓe.
“Wannan batu na yaƙin neman zaɓe kafin hukumar INEC ta ba shi dama, gwamnatin wancan lokacin ce ta fara yin hakan, wanda kuma hakan ke nuni da cewa; hukumar INEC ba za ta iya yin alƙalanci na gaskiya da adalci ba,” in ji shi, inda ya ƙara da cewa; jam’iyyun adawa sun “Faɗa tarkon” APC ta hanyar shiga yaƙin neman zaɓe da wuri.
Har ila yau, a zaɓen cike gurbi na baya-bayan nan, Galadima ya yi watsi da nasarar da APC ta samu, inda ya yi misali da Jihar Kano da Zamfara, musamman ganin yadda jami’an tsaro suka tsorata masu kaɗa kuri’u”.
Ya ƙara da cewa, “Ba su ci zaɓe ko guda ɗaya ba, amma sun sanar a matsayin su ne waɗanda suka lashe zaɓen. A mazaɓar Bagwai da Shanono, mun samu ƙuri’a 16,000; yayin da APC ta samu ƙuri’a 5,000. A wata ƙaramar hukumar kuma, NNPP ta samu sama da ƙuri’a 5,700, yayin da APC kuma ta samu ƙuri’a 265 kacal.
“Sama da sojoji 30,000 aka kai Zamfara, domin aiwatar da zaɓukan mazaɓu biyar kacal. An yi wa mutane dukan tsiya, an nakasa wasu, an kori wasu, sannan a ƙarshe sun rubuta wa kansu sakamakon zaɓen tare kuma da bayyanawa.”
Dangane da irin ƙarfin da jam’iyyar NNPP ke da shi, Galadima ya bayyana cewa; Shugabanta Rabiu Musa Kwankwaso, ba shi da abokin karawa idan ana batu na tasiri a siyasance.
“Kwankwaso shi ne babban jigon siyasar Nijeriya, domin kuwa shi kaɗai ne, wanda tauraronsa yake haskawa; saboda haka, idan har za a yi zaɓe na gaskiya, shi ne mafi farin jini a Nijeriya,” in ji shi.
Haka zalika, ya yi watsi da rahotannin da ke cewa; Kwankwaso ya gana da shugaba Bola Tinubu kwanan nan.
“Ƙarya ne batun cewa, Kwankwaso ya gana da Tinubu a Faris. Ai wannan cin fuska ne ma, ta yaya za ka yi wa wanda ya ayyana ka a matsayin maƙiyi aiki?” Ya ƙara da cewa, NNPP ta kori waɗanda suka yi iri wannan ta’asa ba tare da amincewar jam’iyyar ba.
Dangane da ƙawancen siyasa kuma, Galadima ya ce; son kai a tsakanin ƴ an adawa, shi ne musabbabin hana haɗin kai a tsakaninsu.
“Zan so dukkaninmu mu haɗu mu ceci wannan ƙasa tamu baki-ɗaya, amma dukkaninmu, mun san wa da wa ya kamata a tsayar a Nijeriya, domin samun nasarar lashe zaɓe?
Ya kuma nuna farin cikinsa da batun tattaunawar da aka samu rahoto cewa, ana yi tsakanin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan da kuma Peter Obi na jam’iyyar Labour Party, inda ya bayyana cewa, “Idan za su iya haɗa kawunansu wuri guda, su fitar da mutum ɗaya; babu shakka ƙasa za ta ɗauki saiti, domin kuwa hakan zai kasance tamkar wata dabara ce ta fitar da mu daga cikin wannan ƙunci da muke ciki.”
Da yake watsi da batun siyasar yanki da shiyya, Galadima ya ce; “Ban yarda da batun siyasar Arewa da Kudu ba. Mafi cancantar ɗan Nijeriya, ko daga ina ya fito, ko da kuwa daga mafi ƙanƙantar yare ne, shi ya kamata a zaɓa.”
Galadima ya kuma goyi bayan yawaitar jam’iyyu, yana mai cewa; ko kaɗan bai kyautu a tauye yawansu a Nijeriya ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yaƙin neman zaɓe Ya ƙara da cewa ya ƙara da cewa Galadima ya
এছাড়াও পড়ুন:
Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe ya kaddamar da aikin samar da wutar lantarki ta hasken rana mai ƙarfin megawat 1 a garin Talasse, karamar hukumar Balanga.
Aikin, wanda aka kulla ta hanyar haɗin gwiwa tsakanin Hukumar Samar da Wutar Lantarki a Karkara (REA), Bankin Duniya, da kamfanin MIDS Dynamics, na da aniyar samar da wutar lantarki ba tare da yankewa ba ga sama da gidaje 8,000 a Talasse da kauyuka makwabta, idan aka kammala shi cikin watanni huɗu.
Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a Indonesia Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800A wajen bikin kaddamar da aikin, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana shi a matsayin muhimmin ci gaba a shirin gwamnatinsa na bunƙasa makamashi mai tsabta, araha da kuma dorewa.
“Wannan aiki ba kawai zai ba da haske ga gidaje ba ne kawai, zai ƙarfafa kasuwanci, ya samar da ayyukan yi, kuma ya kawo ci gaban tattalin arziki a yankin,” in ji Gwamnan.
Ya ƙara da cewa aikin ya nuna nasarar haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu wajen ci gaban fannin makamashi, tare da yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa gyare-gyaren da yake kawo wa fannin wutar lantarki, musamman Dokar Wuta ta 2023, wadda ta bai wa jihohi damar tsara hanyoyin samar da makamashinsu.
Shugaban REA, Injiniya Abba Aliyu, ya jinjina wa Gwamna Inuwa bisa hangen nesa da jajircewarsa wajen inganta makamashi a jihar, inda ya ce hukumar na shirin aiwatar da ƙarin ayyukan sola a ƙananan hukumomi 10 na jihar.
A nasa bangaren, Shugaban MIDS Dynamics, Injiniya Halis Mohammed, ya bayyana Gombe a matsayin jiha ta farko a Najeriya da ta bayar da kuɗin haɗin gwiwa don irin wannan aiki, kuma jagora a sauyin makamashi.
Shugabannin yankin, ciki har da Bala Waja, Alhaji Mohammed Danjuma Mohammed, da Dan Majalisa Musa Buba, sun gode wa Gwamnan bisa cika alkawarin da ya ɗauka, tare da alƙawarin kare aikin daga lalacewa da satar kayan aiki.
“Mun daɗe muna jiran wannan rana. Yanzu haske ya dawo cikin ƙasar Waja,” in ji ɗaya daga cikin shugabannin yankin.