’Yan bindiga sun kashe basarake, sun tarwatsa mutane a Sakkwato
Published: 20th, September 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga da ake zargin Lakurawa ne, sun kai hari ƙauyen Sayinna, da ke Ƙaramar Hukumar Tangaza a Jihar Sakkwato.
Sun kashe Hakimin ƙauyen, Malam Murtala Sa’adu, tare da wani mutum mai suna Ibrahim Mai-Kuɗi.
Yadda za ka dawo da kuɗinka da ka yi kuskuren turawa wa wani An tsinci gawar kwamandan hukumar NDLEA a otel a KalabaMai bai wa shugaban Ƙaramar Hukumar Tangaza shawara, Alhaji Gazali Raka ne, ya tabbatar da harin.
Ya ce maharan sun kashe hakimin ne saboda yana taimaka wa ’yan sa-kai wajen tsaro a yankin.
An ce maharan sun shiga ƙauyen ne da misalin ƙarfe 1:30 na daren ranar Alhamis, inda suka dinga harbi a ko ina.
Bayan sun kashe mutanen biyu, sai suka tsere zuwa cikin daji.
Sojojin Operation FANSAN YANMA sun isa yankin, inda suka ɗauki gawarwakin zuwa asibiti.
Rahotanni sun nuna cewa Lakurawa sun kai hare-hare a wasu ƙauyuka na ƙananan hukumomin Kebbe da Tambuwal, inda suka ƙone gidaje, suka kwashe kaya, kuma suka tilasta mutane yin gudun hijira.
A ƙaramar hukumar Kebbe, ƙauyuka kamar Fakku, Sha’alwashi, Tulluwa, Bashi Bakin Dutse da Rafin-Gora sun zama kufai saboda mutane sun tsere.
Hakimin Fakku da iyalansa sun bar garin, sun tsere zuwa Koko a Jihar Kebbi, inda suka haɗu da ɗaruruwan ’yan gudun hijira daga yankin.
Matsalar tsaro a Jihar Sakkwato na ƙara ta’azzara, kuma jama’a na kira gwamnati ta ɗauki matakan gaggawa don kawo ƙarshen lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hari Lakurawa Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
Da yake kaddamar da shirin, Darakta Janar na IRM, Alhaji Anas Muhammad, ya ce an kirkiro da shirin ne domin karfafa zaman lafiya da hadin kai ta hanyar tallafa wa Musulmai da Kiristoci ta bangaren samar da kiwon lafiya da bayar da tallafin kayan abinci da jari.
Ya ce: “Kalubalen lafiya ba sa bambance addini ko kabila, don haka bama bambantawa wajen bayar da tallafin. in sha Allah zamu ci gaba da aiwatar da irin wannan shiri a fadin jihar Kaduna baki daya.”
A nasa jawabin, Shugaban hukumar KADCHMA, Malam Abubakar Hassan, ya bayyana cewa wannan hadin gwiwa tana nuna muhimmancin dangantaka tsakanin gwamnati da kungiyoyi masu zaman kansu wajen cimma dorewar tsarin inshorar lafiya ga kowa.
Ya kara da cewa kaddamar da inshorar lafiya kyauta na shekara guda babban ci gaba ne a cikin gyaran fannin lafiya da ake gudanarwa a jihar, inda ya yaba da kokarin gidauniyar IRM wajen tallafawa rayuwar al’ummar Kaduna – Musulmai da Kiristoci.
Wasu daga cikin wadanda suka amfana da shirin daga Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) reshen Kaduna da kuma kungiyar ci gaba ta Darikar Tijjaniyya ta jihar Kaduna sun bayyana farin ciki da godiya ga gidauniyar da kuma gwamnatin jihar, inda suka ce inshorar lafiya kyauta za ta rage musu nauyin kashe kudin magani tare da karfafa hadin kai a tsakanin al’umma da samar da zaman lafiya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA