HausaTv:
2025-09-20@20:38:05 GMT

Iran za ta katse hulda da IAEA idan aka maida mata takunkuman MDD

Published: 20th, September 2025 GMT

Iran ta yi gargadin cewa za ta kawo karshen duk wata yarjejeniyarta da hukuar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, muddin ake sake dawo mata takunkuman MDD.

Kwamitin koli na tsaron kasar Iran ya ce Tehran za ta dakatar da hadin gwiwar da take yi da Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) bayan da Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kada kuri’ar dage takunkumin da aka kakabawa Tehran na dindindin.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya Asabar, babban jami’in tsaron kasar Iran ya yi Allah wadai da matakin “marasa hankali” da Birtaniya, Faransa, da Jamus –wanda aka fi sani da E3– game da shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran cikin lumana

Mataimakin ministan shari’a da harkokin kasa da kasa na kasar Iran Kazem Gharibabadi ne ya bayyana hakan, inda ya ce yarjejeniyar da aka cimma a baya-bayan nan tsakanin Tehran da hukumar ta IAEA a birnin Alkahira za ta kawo karshe idan Majalisar Dinkin Duniya ta kakaba mata takunkuman, da ake kira “snapback” a turance.

Kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya yi watsi da matakin bayan da ya kasa samun kuri’un da suka dace.

“kasashen Sin da Rasha sun bayyana cewa, matakin da wadannan kasashe uku suka dauka ya sabawa doka.”

A ranar 9 ga watan Satumba ne ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da darakta janar na hukumar IAEA Rafael Grossi suka cimma matsaya kan tsare-tsare masu amfani na maido da hadin gwiwa bayan wata ganawa da suka yi a birnin Alkahira na kasar Masar.

Wannan mataki dai ya biyo bayan amincewar da majalisar dokokin kasar Iran baki daya ta amince da wata doka da ta bukaci Iran ta dakatar da duk wani hadin gwiwa da hukumar ta IAEA, biyo bayan harin da Amurka da Isra’ila suka kai kan cibiyoyin nukiliyar kasar guda uku, wanda ya sabawa dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya ta NPT.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Venezuela ta bukaci MDD ta binciki harin da Amurka ta kai a yankin Caribbean September 20, 2025  Spain za ta hada kai da kotun ICC domin gudanar da bincike kan laifukan da Isra’ila ta aikata a Gaza September 20, 2025 Falasdinawa 47 sun yi shahada a Hare-haren Isra’ila September 20, 2025 Sudan: Rundunar Daukin Gaggawa ( R.S.F ) Ta Kashe Mutane 75 A Wani Hari Da Ta Kai Wa Masallaci A Garin Al-Fasha September 20, 2025 Pakistan: Makaman Nukiliyarmu Suna Cikin Yarjejeniyar Tsaro Da Mu Ka Kulla Da Saudiyya September 20, 2025 Adadin Falasdinawa Da HKI Ta Kashe Da Jikkatawa Sun Haura 230,000 September 20, 2025  Sheikh Na’im Kassim Ya Kira Yi Saudiyya Da Ta  Bude Sabon Shafi Da Gwagwarmaya September 20, 2025 Arqchi: Iran Ba Ta Amince Da Duk Wani Matakin Matsin Lamba Da Rashin Adalci Ba September 20, 2025 Jakadan Iran A MDDuniya Ya Ce: Kwamitin Sulhu Ya Rasa Damar Tattaunawa Da Fahimtar Juna September 20, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Jaddada ‘Yancin Kasar Na Mayar Da Martani Kan Sabawa Doka September 20, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Adadin Falasdinawa Da HKI Ta Kashe Da Jikkatawa Sun Haura 230,000

Kididdigar da aka fitar akan adadin Falasdinawan da su ka yi shahada da kuma jikkata sun haura 230,000,wanda ya faro tun daga watan oktoba 2023.

Ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ce ta fitar da wannan kididdigar a jiya Juma’a, sannan kuma ta bayyana cewa an kara samin wani adadi mai yawa na shahidai a cikin sa’oi 24, yayin da wasu 146 su ka jikkata.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza din ta kuma bayyana cewa; Da akwai ma’aikatan agaji da suke aiki tukuru domin fito da shahidan da suke kwance a karkashin baraguzai.

A fagen yunwa da take ci gaba da daukar rayukan mutanen Gaza kuwa, ma’aikatar kiwon lafiyar ta Gaza, ta ce, an sami Karin wasu shahidai 4 da yunwa ta kashe da hakan ya kai adadinsu zuwa 440,daga cikinsu da kananan yara 147.

A nata gefen, hukumar kiwon lafiya ta duniya ( w.h.o) ta yi gargadi akan durkushewar cibiyoyin  kiwon lafiya a yankin saboda rashin kayan aiki da makamashi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka  Sheikh Na’im Kassim Ya Kira Yi Saudiyya Da Ta  Bude Sabon Shafi Da Gwagwarmaya September 20, 2025 Arqchi: Iran Ba Ta Amince Da Duk Wani Matakin Matsin Lamba Da Rashin Adalci Ba September 20, 2025 Jakadan Iran A MDDuniya Ya Ce: Kwamitin Sulhu Ya Rasa Damar Tattaunawa Da Fahimtar Juna September 20, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Jaddada ‘Yancin Kasar Na Mayar Da Martani Kan Sabawa Doka September 20, 2025 Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Mayar Da Martani Kan Zargin Shugaban Kasar Faransa September 20, 2025 Shugaban Kasar Faransa Zai Amince Da Kasar Falasdinu A Ranar Litinin Mai Zuwa A Birnin New York September 20, 2025 Tinubu Zai Dauki Nauyin Gasar Wasanni Commonwealth A 2030 September 19, 2025 Kungiyar Tarayyar Turai EU Ta Mika Bukatunta Ga Kasar Iran. September 19, 2025 Dakarun Sojin Yamen Su Kai Hare-hare A Muhimman Wurare A HKI. September 19, 2025 Isra’ila Na ci Gaba Da Kutsa Kai A Tsakiyar Gaza A Yau Juma’a September 19, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Adadin Falasdinawa Da HKI Ta Kashe Da Jikkatawa Sun Haura 230,000
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Jaddada ‘Yancin Kasar Na Mayar Da Martani Kan Sabawa Doka
  • Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Mayar Da Martani Kan Zargin Shugaban Kasar Faransa
  • Shugaban Kasar Faransa Zai Amince Da Kasar Falasdinu A Ranar Litinin Mai Zuwa A Birnin New York
  • Kungiyar Tarayyar Turai EU Ta Mika Bukatunta Ga Kasar Iran.
  • Amurka Ta Yi Amfani Da Kujeran Veto Don Hana Zaman Lafiya A Gaza
  • Husi: Kai Wa Kasar Katar Hari Gargadi Ne Ga Al’ummar Musulmi
  • Shugaban Kasar Iran Ya bayyana Yadda Hadin Gwiwa Tsakanin Iran Da Rasha Ya Kawo Ci Gaba Tsakaninsu
  • Eslami: Dole ne IAEA ta zama mai cikakken ‘yancin cin gashin kai