Aminiya:
2025-09-24@08:35:39 GMT

Burkina Faso, Mali da Nijar sun fice daga Kotun ICC

Published: 23rd, September 2025 GMT

Ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar da sojoji ke mulki sun sanar cewa sun fice daga Kotun Duniya ta Hukunta Manyan Laifuka (ICC).

A sanarwar da suka fitar ranar Litinin sun bayyana ICC a matsayin “kayan aikin mulkin mallaka na zamani.”

Ƙasashen ukun, waɗanda aka yi juyin mulki a cikinsu tsakanin shekarun 2020 zuwa 2023, sun kafa ƙawance mai suna Kungiyar Kasashen Sahel (AES) domin haɗa kai da nisantar da kansu daga ƙasashen Yamma, musamman tsohuwar mai mulkinsu, Faransa.

A cikin sanarwar haɗin gwiwa da suka fitar, ƙasashen sun ce kotun da ke birnin Hague “kayan aikin danniya ce a hannun masu mulkin mallaka.”

’Yan sanda sun kama mutum 4 kan kai wa Lakurawa babura a Kebbi Faransa ta amince da ’yancin ƙasar Falasɗinu a hukumance

Sun ƙara da cewa, “ICC ta kasa tabbatar da shari’o’in manyan laifuka da suka haɗa da laifukan yaƙi, kisan gilla ga bil’adama, kisan ƙare dangi da kuma laifukan cin zarafin ƙasa.”

Sun ce suna shirin kafa “hanyoyin cikin gida domin tabbatar da zaman lafiya da adalci.”

Doka ta tanadar cewa ficewar kowace ƙasa daga ICC zai fara aiki ne shekara guda bayan an miƙa sanarwar ficewar ga Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya.

Tun bayan kafa AES, Burkina Faso da Mali da Nijar sun ƙara kusanci da ƙasashe irin su Rasha, wadda Shugabanta Vladimir Putin ke fuskantar sammacin kame daga ICC tun watan Maris 2023 kan yaƙin da ake yi a Ukraine.

Sai dai ƙasashen ukun na fama da hare-haren ta’addanci daga ƙungiyoyin masu alaƙa da Al-Qa’ida da Daesh, yayin da ake kuma zargin sojojinsu da aikata laifuka kan fararen hula.

Kotun ICC dai an kafa ta ne a 2002 domin gurfanar da waɗanda suka aikata manyan laifuka — musamman na yaƙi — a inda gwamnati ba ta da ikon ko kuma ba ta da niyyar ɗaukar mataki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijar

এছাড়াও পড়ুন:

Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina

Ƙaramar Hukumar Sabuwa da ta Ɗandume a Jihar Katsina sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, a wani yunƙuri na kawo ƙarshen hare-hare, kashe-kashe da sace-sacen da suka daɗe suna addabar yankin.

An gudanar da taron sulhun ne a ranar Asabar a ƙauyen Kabalawa Dungun Mua’zu, da ke iyaka da ƙananan hukumomin biyu, amma yana ƙarƙashin Sabuwa.

Da wannan ci-gaban, adadin ƙananan hukumomi da suka ƙulla yarjejeniyar sulhu da ’yan bindiga a jihar ya kai tara.

Sauran sun haɗa da Batsari da Kankara, Kurfi da Musawa da Ɗanmusa da Jibia da kuma Faskari.

Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyu NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu

Shugaban Ƙaramar Hukumar Sabuwa, Sagir Tanimi, da takwaroransa na Ɗandume, Bashir Gyazama, sun halarci taron, inda aka ce su ne suka taimaka wajen cimma yarjejeniyar.

Taron wanda ya ɗauki sa’o’i da dama ya haifar da wasu muhimman matsaya da ɓangarorin biyu suka cimma.

An amince da dakatar da kai hari, inda ’yan bindiga suka yi alƙawarin daina kai hare-hare a ƙauyuka.

Haka kuma an ba su damar shiga garuruwa da ƙauyuka domin harkokin kasuwanci ba tare da tsoron cutarwa daga jama’a ba.

Bugu da ƙari, ’yan bindigar sun yi alƙawarin sako mutanen da suka yi garkuwa da su, sai dai sun roƙi gwamnati ta yi ƙoƙarin ganin an saki ’ya’yansu da ke tsare.

Ɓangarorin biyu sun kuma sha alwashin yin aiki tare domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

A yayin taron, ’yan bindiga da dama sun halarta ɗauke da manyan makamai, tare da shugabanninsu da suka haɗa da Idi Muwage da Alhaji Kabiru da Kachalla Rusku da Kachalla Murtala da Kachalla Mai Saje da Kachalla Dawa da Ardo Abdulsalam Fatika da kuma Alhaji Labi.

Shugaban kwamitin zaman lafiya, Dakta Salisu Ladan, ya bayyana cewa manufar yarjejeniyar ita ce dawo da zaman lafiya mai ɗorewa da kawo ƙarshen kashe-kashe da garkuwa da mutane da sauran munanan ayyuka.

Ya ƙara da cewa, “Shugabannin yankin sun tabbatar wa ’yan bindigar da tsaron rayukansu tare da maraba da su don su ci gaba da gudanar da harkokin kasuwanci a kasuwannin yankin.”

Haka kuma an cimma matsaya cewa za a buɗe kasuwar shanu ta Ɗandume da aka rufe saboda matsalar tsaro, domin bai wa ’yan bindigar damar kawo dabbobinsu da yin ciniki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Afirka Uku Sun Sanar Da Ficewa DagaKotun Hukunta Manyan Laifuka Ta Duniya
  • Kotun Indiya ta daure dan Najeriya shekara 10 kan safarar miyagun kwayoyi
  • An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • Bayan Mutuwar Wani Matashi, An Kafa Dokar Ta Baci A Yauri
  • Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina
  • Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa
  • Hatsarin mota ya yi ajalin mutum 4, 16 sun jikkata a Yobe
  • Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?